Addini
Abinda yasa ake hawa dutsen Dala rana Takutaha

Hakika hawa dutsen Dala a ranar da ake gabatar da bikin takutaha yana nuna alamun bikin Maguzawa da suke yi a Kano duk shekara, wanda suke hawa dutsen Dala da Gwauron Dutse da Magwan da Fanisau suna gabatar da bukukuwan bauta.
Ganin cewa shi kansa bikin takutaha, malaman Madabo sun qirqire shi ne domin kawar da hankalin matasa da mata daga wadannan bukukuwa na Maguzawa, to da alamun shi ya sa har yanzu a duk ranar bikin takutaha samari da mata da yara suke yin dandazo wajen hawa wannan dutse na Dala.
Duk da cewar su Maguzawa suna gabatar da bautarsu ne bisa jagorancin shugabansu, wato Barbushe wanda yake shiga xakin Tsumburbura ya jiyo musu abin da zai faru a wannan shekarar, kuma ya fito ya sanar da su.

Hoto daga Dutsen Dala a bikin Takutaha na bana
A yanzu ba haka ba ne, domin kuwa sai bayan an gama karatun Madabo kuma babban malami ya yi addu’a an watse. A sannan ne yara da samari suke tafiya domin hawa dutsen Dala. Don haka, ba sharaxin bikin ba ne sai an hau wannan dutsen.
A kan Dala, ana gabatar da abubuwa ne da suka shafi nishaxantarwa da kuma kallon qwaryar birnin Kano. Wasu har hotuna suke xauka. Daga baya, an samu cewar wasu ma suna hawa ne domin su yi shaye-shayen kayan maye da yin caca da kuma faxace-faxacen ‘yan daba wanda har ta kan kai da ji wa kai rauni. Wannan ba ya rasa nasaba da nason irin yadda maguzawan da suke yin bikinsu a kan dutsen Dalan suke yin shaye-shayen giya da sauransu. Don haka, ana iya kallon wannan gurvacewa a matsayin yadda bikin maguzawan na asali yake a gurvace.

Hoto daga Dutsen Dala a bikin Takutaha na bana
Matsayin Bikin Takutaha
Bikin takutaha muhimmiyar rana ce a cikin garin Kano, domin a wannan rana akan yanke duk wasu hulxoxi a mayar da hankali wajen gudanar da wannan biki, musamman a wajen qananan yara. Dangane da wannan biki kuwa, waxansu suna ganin ba zai rasa alaqa da bautar gunkin Tsumburbura ba, wanda jama’ar Kano suke yi tun kafin zuwan addinin Musulunci (Ibrahim,1982:290). Bukukuwan da Maguzawa suke yi a kan dutsen Dala yana matuqar jan hankalin mata da yara da baqi, don haka sai malaman Madabo suka haxu a masallacin Madabo suka shawarta kan yadda za su xauke hankalin masu zuwa kallon waxannan bukukuwa na Maguzawa.
Manya-manyan malaman wannan zamani da suka zartar da wannan shawara, sun haxa da: Shehu Isa Mai Lawali da Shehu Mamuda mai Mudawwana da Shehu Ibrahim Liman Mai batta da Shehu Sulaiman mai rubutu da sauransu. Haka kuma, an sami wakilcin malamai daga unguwannin Dukurawa da Sheshe da Mandawari da Jujin-‘yanlabu da Maxatai da sauransu (Hassan,1998:97).

Hoto daga Dutsen Dala a bikin Takutaha na bana
Matsayin bikin Takutaha bai wuce ganin an kawar da hankalin yara da mata daga aqidar Maguzanci zuwa tarbiyyar musulunci ba. Wannan shi ne dalilin da ya sa Madabo suka kafa yin Mauludi a wannan unguwa, wanda daga baya ne mutane suka sauya masa suna zuwa Takutaha.
Dangane da sauran al’umma kuwa, wannan rana tana da matsayi sosai a wajensu. A wannan rana sukan sami damar ziyartar dangi waxanda aka daxe ba a haxu ba. Baya ga haka, qananan yara sukan sami walwala da nishaxi a wannan rana, musamman a kan Dala, inda ake kaxe-kaxe da raye-raye. Har wa yau, masu kayan sayarwa suna samun ciniki sosai, kasancewar jama’a suna zuwa daga vangarori daban-daban. Bugu da qari, al’umma suna haxuwa don yi wa kawunansu da garinsu addu’o’i baki daya.
Rubutu masu alaka:
Fitattun hotuna daga bikin Takutaha na bana
Yadda ake gudanar da bikin Takutaha a Kano
Kun san menene ma’anar Takutaha?
Marubuci: Tijjani Shehu Almajir
+234(0)8035943092
Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Bayero, Kano.

Addini
Hukumar Shari’a ta shirya buɗe baki ga Mutanen da suka musulunta a Kano

A ƙoƙarin ta na ƙara ɗaɓɓaƙa harkokin addinin Musulunci, hukumar Shari’ah ta jihar Kano da haɗin guiwar kungiyar World Assembly of Muslim Youth (Wamy), sun shirya wa waɗanda suka karbi addinin Musulunci shan ruwa a ranar Lahadi 23 ga Ramadan shekarar 1446.
Taron shan ruwan dai ya gudana ne a harabar hukumar karkashin Jagorancin Mukaddashin Shugaban ta Sheikh Ali Ɗan Abba.
Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Muƙaddashin Daraktan yaɗa labarai na hukumar shari’a ta jihar Kano, Musa A Ibrahim (Best Seller).
Hukumar Shari’ar ta kuma ayyana ranar 15 ga Ramadan domin ta zama ranar da za ta rinƙa shan ruwa da waɗanda suka karɓi addinin Musulunci da za a rinƙa yi a duk shekara.
“Muna kuma miƙa godiya ga gwamnatin jihar Kano a karkashin gwamna Abba Kabir Yusuf, da ƙungiyar World Assembly of Muslim Youth [WAMY] da suka ba mu gudummawa wajen shirya wannan taron, “in ji Sheikh Ali”.
Taron shan ruwan dai ya sami halartar dukkanin shugabannin hukumar da mambobin ta da kuma ma’aikatanta tare da shugabannin kungiyar WAMY, da wasu manyan mutane da suka halarta.
Da yake nasa jawabin wakilin shugaban kungiyar Wamy Alhaji Sanusi, ya nuna jin daɗinsa da yadda wannan shan ruwa ya gudana, kuma ya tabbatar da cewar kungiyar su ƙungiya ce ta taimakon addinin musulunci da musulmi a ko ina suke, kuma kungiyar zata ci gaba da wannan aikin alherin da izinin Allah S.W.T.

Addini
Ku taimakawa mabuƙata da Naman Sallah bisa halin matsin rayuwar da ake ciki – Limami

Babban limamin masallacin juma’a na Alaramma Abubakar Ɗan Tsakuwa, da ke unguwar Ja’en Ring road Mallam Abdulkareem Aliyu, ya yi kira ga al’ummar Musulmi, da su kiyaye ƙa’idojin yanka Dabbobin Layyah, domin gujewa cin mushen Nama.
Mallam Abdulkareem Aliyu, ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u, lokacin da yake tsokacin huɗubar da ya gabatar ranar Sallar Idin da ya jagoranta a masallacin ranar Lahadi 17 ga watan Yunin 2024.
Ya ce a mafi yawan lokuta al’umma sukan yanka dabbobi amma rashin bin ƙa’idojin yanka yakan sanya wa su ci mushen nama ba tare da sun sani ba, a dan haka su tashi tsaye wajen sanin yadda ake yanka Dabbobin a mahanga ta addinin Musulunci.
A cewar sa, “Musulmai ku kwaɗaitu da yin sadakar naman layya musamman ma ga masu ƙaramin ƙarfi domin rabauta da rahamar Ubangiji S.W.T, “in ji shi”.
Mallam Abdulkareem Aliyu, ya kuma ce, akwai buƙatar a kiyaye nau’ikan dabbobin da aka sahale ayi layya da su, waɗanda suka haɗar da nau’in Sa ko Saniya, da kuma Raƙumi ko Raƙuma (Taguwar), ko kuma Rago ko Tinkiya, ko Akuya ko kuma Ɗan Akuya.
Wannan dai na zuwa ne bayan da al’ummar Musulmin Duniya suka gudanar da babbar Sallah, a jiya Lahadi 16 ga watan Yunin shekarar 2024.

Addini
An ga jinjirin watan Zul-Hijjah a Najeriya, ranar Lahadi 16 ga watan Yuni Babbar Sallah

Fadar mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Abubakar Sa’ad na uku, ta sanar da ganin jinjirin watan Zul-Hijjah na shekarar 1445.
Hakan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da fadar Sarkin Musulmin ta fitar, mai ɗauke da sa hannun Wazirin Sakkwato, kuma shugaban kwamitin duban wata Farfesa Sambo Wali Junaid.
Sanarwar ta kuma ce duba da ganin jaririn watan na Zul-Hijjah da akayi a jiya Alhamis, hakan ya tabbatar da cewar yau Juma’a ɗaya ga watan Zul-Hijjah, wanda za’ayi babbar Sallah a ranar Lahadi 16 ga watan Yunin 2024.
Tun dai a jiya Alhamis hukumomi a ƙasar Saudiyya suka sanar da ganin Jaririn watan na Zul-Hijjah, lamarin da ya kasance za’ayi tsayuwar Arafa a ranar Asabar 15 ga watan Yunin 2024, yayin da za’ayi babbar Sallah a ranar Lahadi 16 ga watan na Yuni.
Kafar Dala FM Kano, ta rawaito cewa, kawo yanzu dai maniyyata aikin hajjin bana da dama ne ke ci gaba da shiga ƙasa mai tsarki, a ƙoƙarin su na zuwa domin sauke Farali.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su