Manyan Labarai
Yadda zaka shigar da korafi akan yan sanda.
A tashin dai zaka iya ganin sa cikin kayan sarki na gaskiya, ma’ana kayan da jami’an yan sanda suke sanyawa yayin da suke bakin aiki.Shaida ta biyu itace katin shaida wato ID card, wanda ya sha banban da sauran katunan hukumomi da aka saba gani. Katin shaida na dan sanda yana dauke da tambarin giwa, sai kuma sunan mai shi da lambar sa, da kuma sa hannun shugaban yan sanda na kasa. Bayan katin kuwa yana dauke ne da bayanan mallaka na rundunar ta kasa, bayanan dake kasancewa iri daya dana jikin kowanne irin katin shaidar da hukumar ke rabawa jamianta.
Yaya zanyi idan jami’in tsaro ya shiga gaban abin hawa na, ko kuma ya kama ni?
Cikin wata tattaunawar mako da muka yi da kakain yan sanda na jihar kano ASP Abdullahi Haruna Kiyawa yau talata, yace hanya da mutum zai bi shine a tashin farko ya nemi sanin wanda ya kama shi, daga wacce tasha ko ofishi na rundunar?Watakila wannan tambaya tazo wa mai jinta da wani sabon al’amari, ko kuma wani yayi tunanin hakan bai yiwuwa ka tambayi hukuma daga inda aka fito.Abdullahi Haruna yace babu wata matsala tunda duk dan sanda, da ya san aikin sa, zai yi faron ciki da jin wannan tambaya daga wanda ya kama, kuma zai bayar da amsa babu bata lokaci.Kakakin yace sanin kowa ne wasu bata gari kan fake da rundunar domin aikata laifukan da zasu bata suna, matukar kuwa al’umma suka nemi sani, to kuwa zasu jefa shakku a zukatan jami’an tsaro na bogi.ASP Abdullahi Haruna yace a yau talata rundunar ta cafke wani dan sanda bogi, wanda yake dauke da katin shaida na hukumar, bayan da ya tare wani mutum domin karbe masa yan kudade. Sai dai bai yi nasara ba tunda wanda aka kama din yayi amfani da nambobin kota kwana, domin neman daukin rundunar, inda nan take suka yi dirar mikiya tare da cafke shi.A cewar sa akwai bukatar al umma suyi amfani da kwarewar neman sanin wajen neman ba’asi daga yan sanda da suka nemi karbar na goro a hannun su, sannan akwai kyutuwar su karbi nambobin waya na ofisoshin yan sanda da jami’an su, musamman wadanda ke kusa dasu domin neman shawarwari da baasi idan suka samu kai a hannun irin wadannan jami’ai.ASP Kiyawa ya bukaci al’umma su ziyarci shafukan sada zumunta na zamani, domin daukar nambobin waya da rundunar ta ajiye domin amfanin al umma. Ko kuma bibiyar ayyukanta kai tsaye a shafukan na twitter, instagram da facebook.Bisa sauye sauye da sabon kwamishinan yan sanda na jihar kano Habu Amadu Sani yazo, kwamishinan ya umarci a dora lambobin baturan yan sandan kananan hukumomi akan manhajar opera, domin amfanin al umma.Haka kuma ya zayyano wasu nambobin hukumar na bangaren kar ta kwana kamar: 08032419754, 08123821575.Haka kuma zaka iya shigar da korafi akan duk wani jami’in dan sanda da ya aikata masa ba dai dai ba akan lambar waya: 09064525249, 08150202029.Haka kuma rundunar tana da akwatun wasiku na gmail akan: kanopolicepubliccomplaintdesk@gmail.comA karshe kakakin na yansandan jihar kano ASP Abdullahi Haruna Kiyawa yace suna karbar korafe korafe da shawarwarin al umma ta cikin wannan shiri domin amfani dasu a zahirance.
Manyan Labarai
Gundura da ake zargi da sarewa Ɗan Bijilante hannu da fasa motar ƴan sanda ya shiga hannu
Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta samu nasarar cafke wani Matashi mai suna Inuwa Zakari ɗan shekara 24, wanda akafi sani da Gundura, wanda ake zargi da sarewa wani Ɗan Bijilante hannu, da kuma fasa motar Ƴan Sanda, da wasu Laifuka
Kakakin rundunar ƴan sandan SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwar da ya aikowa Dala FM a daren Litinin, Kiyawa ya ce Matashi Gundura sun daɗe suna neman sa ruwa a jallo bisa zargin sa da tarin Laifuka.
“Gundura ya kasance abokin fitaccen ɗan Dabar nan Abba Burakita ɗa unguwar Ɗorayi da ya rasu a baya, kuma har kotu ma muka gurfanar da shi daga baya ya fita amma bai dai na abinda ya ke yi ba, a ranar zaɓen ƙananan hukumomin Kano, da ya shigo yana yunƙurin tayar da hankalin al’umma jami’an mu suka kama shi, “in ji SP Kiyawa”.
Har ila yau, Abdullahi ya ce an kama Gundura da wukake guda biyu a wani waje na matattarar Yan Daba da suke kira “Jungle” a Unguwar Dorayi.
Rundunar ƴan sandan ta ce ta kuma cafke ƙarin wasu matasa 14, da ake zargin su da aikata maban-banta laifuka, inda aka kama su a tsakanin 25 ga zuwa 27 na watan Oktoban 2024.
SP Kiyawa ya ƙara da cewa yanzu haka waɗanda ake zargin ana ci gaba da bincike a kan su a babban sashin binciken manyan laifuka na CID, da ke hedikwatar rundunar da ke Bompai a Kano, kuma da zarar an kammala za’a gurfanar da su a gaban kotu.
Manyan Labarai
Ku zauna lafiya yayin zaɓen ƙananan hukumomin da ake gudanarwa a Kano – Kwankwaso
Tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi kira ga al’umma da su tabbatar da an samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a zaɓen ƙananan hukumomin da ake gudanarwa yau a Kano.
Sanata Kwankwaso ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kaɗa ƙuri’a a mazaɓar sa ta Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a Kano.
Ya kuma ce akwai buƙatar al’ummar jihar su fita rumfunan zaɓen su kaɗa ƙuri’un su domin ƙara inganta Demukuraɗiyya a jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya.
Kwankwaso ya kuma jaddada wa al’ummar jihar cewar gwamnatin Kano za ta ci gaba da ayyukan alheri a faɗin jihar, domin samar da ci gaban Jama’a.
A ranar Asabar ɗin nan ne dai ake gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar Kano 44, wanda shugabannin fa za’a zaɓa za su shafe tsawon shekaru uku-uku a karagar mulki.
Kafin wannan rana an dai samu cece-kuce akan batun zaɓen, wanda a ranar Talatar da ta gabata wata babbar kotun tarayya da ke jihar Kano, ta dakatar da shugabancin hukumar zaɓen ta jihar Kanseic, da umartar Ƴan sandan jihar su ƙairacewa shiga aikin zaɓen.
Ko da dai a jiya Juma’a babbar kotun jahar Kano ƙarƙashin mai Shari’a Sunusi Ado Ma’aji, ta umarci hukumar zaɓen ta gudanar da zaɓen a yau Asabar, tare da umartar Ƴan sandan su shiga aikin zaɓen, ko da dai wasu mazauna jihar sun shaidawa Dala FM cewar, ba su ga jami’an ƴan sanda ba a wuraren zaɓen.
Jami’an tsaron da aka gani sun haɗar da ƴan Karota, da na Hisbah, da kuma ƴan Bijilante, da jami’an rundunar tsaro da ke yaƙi da ƙwacen Waya da faɗan Daba da magance Shaye-shaye ta Anty Snaching Phone da ke Kano.
Manyan Labarai
Har yanzu jam’iyyu 6 ne suka cika ƙa’idar zaɓen ƙananan hukumomin da za a gudanar kuma babu APC a ciki – KANSEIC
Hukumar zaɓe ta jihar Kano (KANSIEC), ta bayyana sunayen jam’iyyu 6 a matsayin waɗanda suka cika ƙa’idar shiga zaben ƙananan hukumomin da za a gudanar ranar Asabar a Kano.
Shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Malumfashi ne ya bayyana hakan jim kaɗan bayan babbar kotun jaha ta tabbatar da halaccin hukumar zaben.
Farfesa Malumfashi ya bayyana cewar jam’iyyun da suka cika ƙa’idar sun haɗar da Jam’iyyar AA, AAC, Accord, ADC, da APM da kuma jam’iyyar NNPP mai mulki a jihar Kano.
Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, shugaban hukumar zaben ya bukaci hukumomin tsaro da su fito su kare rayuka da dukiyoyin al’umma a lokacin gudanar da zaben, kamar yadda babbar kotun jaha ta umarce su a hukuncin da ta yi da ranar Juma’a 25 ga watan Oktoban 2024.
A ranar Alhamis dai an jiyo yadda kwamoshina mai kula da harkokin yaɗa labarai da al’amuran Shari’a na hukumar zaɓe ta jihar Kano Kanseic, Lawan Badamasi, ya ce za su yi amfani da jami’an tsaron cikin gida domin samar da tsaro yayin zaɓen.
Ya ci gaba da cewa daga cikin jami’an tsaron cikin gidan akwai irin su ƴan Karota, da na Hisbah, da kuma Ƴan Bijilante, domin samar da tsaro idan ƴan sanda suka ƙauracewa shiga aikin zaɓen kamar yadda suka samu umarnin hakan daga wata babbar kotun tarayya da ke jihar Kano.
-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su