Manyan Labarai
Yadda zaka shigar da korafi akan yan sanda.

A tashin dai zaka iya ganin sa cikin kayan sarki na gaskiya, ma’ana kayan da jami’an yan sanda suke sanyawa yayin da suke bakin aiki.Shaida ta biyu itace katin shaida wato ID card, wanda ya sha banban da sauran katunan hukumomi da aka saba gani. Katin shaida na dan sanda yana dauke da tambarin giwa, sai kuma sunan mai shi da lambar sa, da kuma sa hannun shugaban yan sanda na kasa. Bayan katin kuwa yana dauke ne da bayanan mallaka na rundunar ta kasa, bayanan dake kasancewa iri daya dana jikin kowanne irin katin shaidar da hukumar ke rabawa jamianta.
Yaya zanyi idan jami’in tsaro ya shiga gaban abin hawa na, ko kuma ya kama ni?
Cikin wata tattaunawar mako da muka yi da kakain yan sanda na jihar kano ASP Abdullahi Haruna Kiyawa yau talata, yace hanya da mutum zai bi shine a tashin farko ya nemi sanin wanda ya kama shi, daga wacce tasha ko ofishi na rundunar?Watakila wannan tambaya tazo wa mai jinta da wani sabon al’amari, ko kuma wani yayi tunanin hakan bai yiwuwa ka tambayi hukuma daga inda aka fito.Abdullahi Haruna yace babu wata matsala tunda duk dan sanda, da ya san aikin sa, zai yi faron ciki da jin wannan tambaya daga wanda ya kama, kuma zai bayar da amsa babu bata lokaci.Kakakin yace sanin kowa ne wasu bata gari kan fake da rundunar domin aikata laifukan da zasu bata suna, matukar kuwa al’umma suka nemi sani, to kuwa zasu jefa shakku a zukatan jami’an tsaro na bogi.ASP Abdullahi Haruna yace a yau talata rundunar ta cafke wani dan sanda bogi, wanda yake dauke da katin shaida na hukumar, bayan da ya tare wani mutum domin karbe masa yan kudade. Sai dai bai yi nasara ba tunda wanda aka kama din yayi amfani da nambobin kota kwana, domin neman daukin rundunar, inda nan take suka yi dirar mikiya tare da cafke shi.A cewar sa akwai bukatar al umma suyi amfani da kwarewar neman sanin wajen neman ba’asi daga yan sanda da suka nemi karbar na goro a hannun su, sannan akwai kyutuwar su karbi nambobin waya na ofisoshin yan sanda da jami’an su, musamman wadanda ke kusa dasu domin neman shawarwari da baasi idan suka samu kai a hannun irin wadannan jami’ai.ASP Kiyawa ya bukaci al’umma su ziyarci shafukan sada zumunta na zamani, domin daukar nambobin waya da rundunar ta ajiye domin amfanin al umma. Ko kuma bibiyar ayyukanta kai tsaye a shafukan na twitter, instagram da facebook.Bisa sauye sauye da sabon kwamishinan yan sanda na jihar kano Habu Amadu Sani yazo, kwamishinan ya umarci a dora lambobin baturan yan sandan kananan hukumomi akan manhajar opera, domin amfanin al umma.Haka kuma ya zayyano wasu nambobin hukumar na bangaren kar ta kwana kamar: 08032419754, 08123821575.Haka kuma zaka iya shigar da korafi akan duk wani jami’in dan sanda da ya aikata masa ba dai dai ba akan lambar waya: 09064525249, 08150202029.Haka kuma rundunar tana da akwatun wasiku na gmail akan: kanopolicepubliccomplaintdesk@gmail.comA karshe kakakin na yansandan jihar kano ASP Abdullahi Haruna Kiyawa yace suna karbar korafe korafe da shawarwarin al umma ta cikin wannan shiri domin amfani dasu a zahirance.

Manyan Labarai
Babu ɗaga Ƙafa tsakanin mu da Ƴan Daba da masu ƙwacen Waya a Kano – Anty Snaching Phone

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Wayoyin jama’a da kuma daƙile Shaye-shayen kayan maye ta Anty Snaching Phone, ta gargaɗi matasan da suke addabar al’umma da faɗan Daba a cikin birnin jihar Kano, da su ƙauracewa hakan domin ba za su saurarawa dukkanin wanda ya faɗa komar su ba.
Kwamandan rundunar tsaron a jihar Kano Inuwa Salisu Sharaɗa, shi ne ya bayyana hakan a zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, ya ce duk wanda suka kama da laifi musamman ma na faɗan Daba, ko ƙwacen waya ko kuma sha da dillancin kayan maye, za a ɗauki tsattsauran mataki akan sa.
“Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da masu ƙwacen Wayoyin jama’a, da Faɗan Daba, da kuma masu Sha da dallancin kayan Maye a jihar Kano, kuma duk wanda mu ka kama sai mun miƙa shi gurin da ya dace don ɗaukar Mataki, “in ji Inuwa Sharaɗa”.
Ya kuma buƙaci iyaye da su ƙara sanya idanu wajen kula akan shige da ficen ƴaƴan su, ta yadda za su zama ababen koyi a tsakanin al’umma.

Manyan Labarai
Za’a hukunta duk ma’aikacin Shari’ar da aka samu da laifi – Babbar Jojin Kano

Babbar jojin Kano mai Shari’a Dije Abdu Aboki, ta jaddada cewar kwamitin ladabtarwa na hukumar Shari’a a jihar, zai hukunta duk wani ma’aikaci a tsagin Shari’a matuƙar aka same shi da laifin cin-hanci da rashawa.
Mai Shari’a Dije Aboki ta bayyana hakan ne a yayin taron ƙarawa juna sani wanda hukumar shari’ar ta gudanar ranar Talata, a ɗakin taro na Murtala Muhammad Library da ke Kano.
Taron an shirya shi ne don tunasar da sabbin ma’aikatan Shari’a, akan nauyin da ya hau kan su don mayar da hankali sosai akan batun gujewa cin-hanci da rashawa.
Babbar mai Shari’ar Dije Abdu Aboki, ta bayyana cewar akwai takaddu masu ɗauke da lambobin wayarta da aka liƙe a bangon kotuna, kuma duk wanda aka yi wa ba dai-dai ba zai iya sanar da ita ta kan lambobin kuma za a dauki mataki akan duk ma’aikacin da aka samu da laifi.
Wakilin tashar Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, a yayin taron taron ma’aikatan Shari’a da al’umma da dama ne suka samu damar halarta.

Hangen Dala
Rashin wuta: Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.
Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.
Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.
Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.
Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.
Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.
Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su