Connect with us

Manyan Labarai

Yadda zaka shigar da korafi akan yan sanda.

Published

on

A tashin dai zaka iya ganin sa cikin kayan sarki na gaskiya, ma’ana kayan da jami’an yan sanda suke sanyawa yayin da suke bakin aiki.Shaida ta biyu itace katin shaida wato ID card, wanda ya sha banban da sauran katunan hukumomi da aka saba gani. Katin shaida na dan sanda yana dauke da tambarin giwa, sai kuma sunan mai shi da lambar sa, da kuma sa hannun shugaban yan sanda na kasa. Bayan katin kuwa yana dauke ne da bayanan mallaka na rundunar ta kasa, bayanan dake kasancewa iri daya dana jikin kowanne irin katin shaidar da hukumar ke rabawa jamianta.

Yaya zanyi idan jami’in tsaro ya shiga gaban abin hawa na, ko kuma ya kama ni?

Cikin wata tattaunawar mako da muka yi da kakain yan sanda na jihar kano ASP Abdullahi Haruna Kiyawa yau talata, yace hanya da mutum zai bi shine a tashin farko ya nemi sanin wanda ya kama shi, daga wacce tasha ko ofishi na rundunar?Watakila wannan tambaya tazo wa mai jinta da wani sabon al’amari, ko kuma wani yayi tunanin hakan bai yiwuwa ka tambayi hukuma daga inda aka fito.Abdullahi Haruna yace babu wata matsala tunda duk dan sanda, da ya san aikin sa, zai yi faron ciki da jin wannan tambaya daga wanda ya kama, kuma zai bayar da amsa babu bata lokaci.Kakakin yace sanin kowa ne wasu bata gari kan fake da rundunar domin aikata laifukan da zasu bata suna, matukar kuwa al’umma suka nemi sani, to kuwa zasu jefa shakku a zukatan jami’an tsaro na bogi.ASP Abdullahi Haruna yace a yau talata rundunar ta cafke wani dan sanda bogi, wanda yake dauke da katin shaida na hukumar, bayan da ya tare wani mutum domin karbe masa yan kudade. Sai dai bai yi nasara ba tunda wanda aka kama din yayi amfani da nambobin kota kwana, domin neman daukin rundunar, inda nan take suka yi dirar mikiya tare da cafke shi.A cewar sa akwai bukatar al umma suyi amfani da kwarewar neman sanin wajen neman ba’asi daga yan sanda da suka nemi karbar na goro a hannun su, sannan akwai kyutuwar su karbi nambobin waya na ofisoshin yan sanda da jami’an su, musamman wadanda ke kusa dasu domin neman shawarwari da baasi idan suka samu kai a hannun irin wadannan jami’ai.ASP Kiyawa ya bukaci al’umma su ziyarci shafukan sada zumunta na zamani, domin daukar nambobin waya da rundunar ta ajiye domin amfanin al umma. Ko kuma bibiyar ayyukanta kai tsaye a shafukan na twitter, instagram da facebook.Bisa sauye sauye da sabon kwamishinan yan sanda na jihar kano Habu Amadu Sani yazo, kwamishinan ya umarci a dora lambobin baturan yan sandan kananan hukumomi akan manhajar opera, domin amfanin al umma.Haka kuma ya zayyano wasu nambobin hukumar na bangaren kar ta kwana kamar: 08032419754, 08123821575.Haka kuma zaka iya shigar da korafi akan duk wani jami’in dan sanda da ya aikata masa ba dai dai ba akan lambar waya: 09064525249, 08150202029.Haka kuma rundunar tana da akwatun wasiku na gmail akan: kanopolicepubliccomplaintdesk@gmail.comA karshe kakakin na yansandan jihar kano ASP Abdullahi Haruna Kiyawa yace suna karbar korafe korafe da shawarwarin al umma ta cikin wannan shiri domin amfani dasu a zahirance.

Manyan Labarai

Kotu ta bada umarni ga jami’an tsaro da hukumar Hisbah kan su dakatar da kama Mansura Isah

Published

on

Babbar kotun tarayya karkashin jagorancin mai Shari’a Abdullahi Liman, ta takadar da hukumar Hisba da kwamishinan ƴan sanda da kuma mataimakin babban Sifeton ƴan sandan kasar nan daga kama Mansura Isa.

Mai Shari’a Liman ya ayyana cewar ya yi hani ga waɗanda akayi karar ko ƴan korensu ko wakilansu, ko kuma wasu masu aiki amadadinsu daga kamawa ko tsorataswa ko gayyata har zuwa lokacin da za’a saurari kowane ɓangaren.

Wannan umarni dai ya samu ne a cikin wata ƙara mai lamba 159/2024, wadda Mansura Isah ta shigar tana karar hukumar Hisba da kwamishinan ƴan sandan jihar Kano.

Kotun ta sanya ranar 15 ga wannan watan dan sauraron kowane bangare a shari’ar.

Continue Reading

Manyan Labarai

Zamu farfaɗo da masana’antun ƙananan hukumomi 44 na jihar Kano – Kwamishina

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce za ta farfaɗo da masana’antun yin saƙa na ƙananan hukumomi 44 da ke faɗin jihar nan, domin samawa matasa aiki ta yadda za su dogara da kansu.

Kwamishinan ciniki da masana’antu na jihar Kano Alhaji Adamu Aliyu Kibiya, ne ya bayyana hakan, yayin da ya ziyarci masana’antar saƙar kayayyaki ta ƙaramar hukumar Kura yau Laraba, domin duba halin da take ciki tare da duba yadda za’a farfaɗo da ita daga dogon suman da ta yi.

Tun dai a lokacin mulkin tsohon gwamnan Kano Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, a shekarar 2014, ne ya samar da injina a masana’antar, amma tsohuwar gwamnatin Kano da ta ganata ta yi watsi da masana’anatar.

Yayin duba masana’antar Kwamishinan cikinki da masana’antu na jihar Kano Alhaji Adamu Aliyu Kibiya, ya kuma bada tabbacin farfaɗo da masana’antar yin saƙar ta ƙaramar hukumar Kura da ma na faɗin jihar nan, domin samawa matasa ayyukan yi.

Da yake yiwa Dala FM Kano, ƙarin bayani babban sakataren ma’aikatar ciniki da masana’antu na jihar Kano, Muhammad Yusuf Ɗan-duwa, ya ce, farfaɗo da masana’antar ta Kura, na zuwa ne bisa ƙokarin gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, da Kwamishinan ma’aikatar Alhaji Adamu Aliyu Kibiya, domin samawa matasa ayyukan yi.

Ya kuma ce yadda tsohuwar gwamnatin da ta gabata ta wofantar da masana’antar tsawon lokaci, a yanzu gwamnatin su za ta yi duk mai yiyuwa, domin ganin an ta ci gaba da aiki ka’in da na’in.

Tun dai a shekarar 2014 ne aka samar da injina a masana’antar, amma tsohuwar gwamnatin da ta gabata ta wofantar da aikin, lamarin da ya sa aikin ya tsaya cak, inda gwamnatin Kano mai ci a yanzu ta ce za ta farfaɗo da ita domin samawa matasa aikin yi, da kuma bunƙasa tattalin arziƙi.

Continue Reading

Manyan Labarai

Mun ware miliyoyin Kuɗi domin biyan ƴan Fansho haƙƙoƙin su – Gwamnan Kano

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya ce gwamnatin sa ta ware Naira biliyan biyar domin biyan ƴan Fansho haƙƙoƙin su bisa la’akari da yadda ake samun matsala wajen biyan su kudaɗen su.

Gwamnan Kano ya yi wannan jawabin ne da safiyar yau Laraba, yayin taron majalisar zartarwa da gwamnatin jihar ta saba yi duk sati, domin tattauna batutuwan da suka shafi gwamnatin jihar Kano.

“Za mu tabbatar an biya dukkanin waɗanda suka dace hakkin su na Fansho, domin su samu damar gudanar da sana’o’in dogaro da kai da za su iya riƙe iyalan su, “in ji Gwamnan”.

Wakilinmu na fadar gwamnatin Kano Umar Abdullahi Sheka ya rawaito cewa, gwamnatin Kano ta ce za ta tabbatar ta magance matsalar rashin ruwa da al’umma suke fuskanta a sassan jihar, domin samar musu da wani sauƙi.

Continue Reading

Trending