Connect with us

Manyan Labarai

Zaman da majalisar dokokin Kano ta yi a yau laraba.

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta ce za ta yi iya bakin kokarinta wajen tabbatar da gyaran dokar kafa hukumar bunkasawa da Kuma samar da tallafi ga bangaren ilimi ta jihar Kano ta shekarar dubu biyu da goma sha Tara Wanda gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya aike mata.

Mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Kano Honarabul Hamisu Ibrahim Chidari ne ya bayyana haka yayin karanta wasikar da gwamnan Kano ya turowa majalisar game da gyaran kudirin dokar hukumar mai taken Kano state education development establishment support bill 2019.

Ya ce matukar aka amince da gyare-gyaren da aka yi ga hukumar aka Kuma amince da shi akan lokaci zai bai wa jihar Kano daman fara cin gajiyar tallafi kan harkokin ilimi daga kungiyoyin ba da tallafi kan harkar ilimi a duniya.

Wakiliyar mu ta majalisar dokokin jihar Kano Khadija Ishaq muhammad ta rawaito cewa, majalisar ta bukaci sanya batun gyaran dokar cikin ayyukan da za ta gudanar a zamanta na gaba.

A bangare guda kuma hukumomin gwamnati na cigaba da bayyana gaban kwamatocin zauren majalisar domin kare kasafin kudin su.

Inda Ma’aikatar kananan hukumomin ta jihar Kano ta gabatar da naira biliyan dari biyu da goma sha shida da miliyan sittin da biyu da dubu dari tara da saba’in da uku da dari daya da talatin da shida da Kwabo arbain da hudu a matsayin kunshin kasafin kudin kananan hukumomin jihar arbain da hudu.

Hakan ya biyo bayan karanta wata wasikar da ma’aikatar kananan hukumomi ta aikewa majalisar mai dauke da sa hannun kwamishinan ta Murtala Sule Garo wanda mataimakin shugaban majalisar Hamisu Ibrahim Chidari ya karanta da safiyar yau laraba.

Ta cikin wasikar ta bayyana cewar ma’aikatar kananan hukumomi tayi la’akari da bukatun al’umma, gabanin amincewa da kididdigar kudaden da ta ke muradin kashewa.

Daga nan ne majalisar ta baiwa kwamitocin ta mai kula da kasafin kudi da na kananan hukumomi wa’adin makwanni hudu suyi nazarin kunshin kasafin kafin su dawo da shi gabanta.

Manyan Labarai

Ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yiwa ma’aikatan ta ci gaban mai haƙan rijiya ne – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Universal Declaration of Human Rights, ta ce ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yiwa ma’aikatan ta, ci gaban mai haƙan rijiya ne, domin ba zai magancewa ma’aikatan matsalolin su ba.

Daraktan ƙungiyar reshen jihar Kano Alhaji Umar Sani Galadanci, ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da wakilinmu na ƴan Zazu Hassan Mamuda Ya’u, a yau Laraba, lokacin da yake tsokaci a kan bikin ranar ma’aikata da ake gudanarwa yau a Najeriya.

Ya kuma ce kasancewar ƙarin albashin ba zai ragewa ma’aikatan wata damuwa ba, sai dai ma ya tunzura ma’aikatan, bai kamata ƙungyoyin ƙwadago su amine da tsirarun ƙarin ba.

“Matukar gwamnatin tarayya za ta rinƙa tunzura ma’aikata da irin wannan tsirarun albashin babu makawa zamu gurfanar da ita a gaban kotu, “in ji Galadanci”.

Umar Sani ya kuma shawarci gwamnatin tarayya da ta lalubo sabbin hanyoyi da za’a ƙarawa ma’aikatan albashi mai tsoka wanda zai rinƙa magance musu wasu matsalolin su na yau da kullum.

Har ila yau, suma ƙungiyoyin ƙwadago a ƙasar nan, sun yi fatali da ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yiwa ma’aikatan ta da kashi 25 cikin ɗari, da kuma kashi 35 a cikin ɗari.

Ƙungiyoyin ƙwadago da dama na NLC, da TUC, da sauran ƙungiyoyi ne suka gudanar da taron ranar ma’aikan a sassan jahohin ƙasar nan.

Continue Reading

Manyan Labarai

Kayan aikin ginin da ya ruftawa magina a Kuntau ba masu inganci ba ne – Cibiyar masu Taswirar Zane-zanen Muhalli

Published

on

Cibiyar masu tasawirar zane-zanen muhalli ta ƙasa reshen jihar kano, tayi Allah wa dai da kayan da akayi wani ginin Bene da shi mai hawa uku, da ya faɗo akan wasu magina a cikin unguwar Kuntau da ke yankin karamar hukumar Gwale a jihar kano.

Mataimakin shugaban ƙungiyar na kasa Arct Ali Mukhtar, ne ya bayyana hakan a lokacin da cibiyar takai ziyara wajen da al’amarin ya faru.

Ya ce dukkanin kayan da aka yi aikin ginin benen da su ba masu inganci ba ne.

A nasa jawabin shugaban cibiyar a nan nano Arct Bashir Hassan Hanga, kira ya yi ga gwamnatin jihar kano, da ta hana duk masu irin wannan gine-gine ba tare da sahalewar hukumar tsara birane ba wato Knupda, ta kuma ɗauki mataki akan mamallakin wannan gini da ya rushe a kan maginan.

Wakilin mu Shamsu Dau Abdullahi ya rawaito cewa dukkanin tawagar cibiyar tsara gine-ginen, sun ce za su ziyarci asibitin Murtala Muhammad, domin duba mutanen da gini ya fadowa da kuma zuwa ta’aziya gidan waɗanda suka rasu su uku.

Continue Reading

Manyan Labarai

Majalisa ta amince da dokar gwajin cutar Ƙanjamau da ta Sikila kafin aure a Kano

Published

on

Majalisar Dokokin jahar kano ta amince da dokar yin gwajin cutar kanjamau da ta Sikila da kuma sauran cututtuka kafin yin aure.

Da yake Jawabi akan kafa dokar, Shugaban Majalisar dokokin jahar kano Alhaji Jibril Isma’il Falgore, ya ce dokar za ta daƙile yaɗuwar cututtuka a tsakanin ma’aurata da yaɗa su ga iyali da ma al’umma baki ɗaya.

Har ila yau, dokar ta ba da damar yin gwajin cututtuka masu haɗari da wuyar magani kafin yin aure, tare da tanadin hukunci mai tsanani ga duk wanda yaƙi yin biyayya ga dokar.

Mataimakin Akawun Majalisar kuma babban Sakatare Alhaji Nasiru Magaji, ne ya gabatar da karatu na uku akan dokar kafin amincewa da ita a ranar Litinin.

Continue Reading

Trending