Connect with us

Manyan Labarai

Rashin takardun gwajin jinin Ango ya janyo amfasa daurin aure a Kano

Published

on

Al’amarin dai ya faru ne a kauyen Bundum mazabar wangara dake karamar hukumar Tofa a jihar Kano, bayan an gabatar da takardar gwajin jinin Amarya wadda ta tabbatar da lafiyar ta, sai limamin daurin auren, Muhammad Lawan ya tambayi cikakkun takardun shedar gwajin jinin Ango waliyan sa suka ce babu, shi kuma limamin, ya ce ba zai daura auren ba har sai inda takardun.

Jin wannan batun ne shima waliyin Amarya mai suna Sani Inuwa da sauran madaura auren suka goyi bayan lallai sai an kawo takardun gwajin jinni na Angon sannan za a daura auren.

Wannan al’amarin dai ya matukar tada hankalin waliyan Ango Kabiru Ibrahim, nan take ya tuntubi Angon Abdurrashid Shehu, nan take ya ce” Ya yi gwajin jinin amma takardar sakamakon ne aka manta ba’a tafi da ita ba wurin daurin auren”. A cewar Ango.

Wannan ya sanya ba a daura auren ba a lokacin har sai da aka jira a akaje aka dauko takardun, aka kuma tabbatar ta lafiyar Angon ce sannan aka daura auren.

Wakilin mu Ibrahim Abdullahi Sorondinki, ya rawaito cewa cikin  ‘yan kwanakin nan a yankin na Tofa, sau biyu aka fasa daurin aure kwata-kwata, bayan an riga an taru, na farko sabida takardar gwajin jini ta nuna cewar Amaryar na dauke da juna biyu, karo na biyun kuma takardar gwajin jinin ta nuna cewar Angon na dauke da cuta me karya garkuwar jiki wato (HIV).

Manyan Labarai

Gwamnan kano Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan dokar gwajin lafiya kafin aure

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sanya hannu a kan dokar da za ta wajabta yin gwajin lafiya gabanin aure a faɗin jihar ta kano baki ɗaya.

A cikin wata sanarwa da ta samu sa hannu kuma ta fito daga ofishin babban daraktan yada labarai na gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa, ta ce an bijiro da dokar gwajin lafiya ne kafin aure, domin rage yawan yaran da ake haihuwa ɗauke da wasu cututtuka da ake iya ɗauka ko kuma gadonsu daga iyaye, kamar irin cutar Sikila da HIV da kuma ciwon hanta.

Rahotanni sun bayyana cewa, hakan na nufin cewa daga yanzu babu wani aure da za’a ɗaura a jihar har nan sai an gabatar da takardar sakamakon gwajin ƙwayoyin halittun gado, da na cutar hanta (Hepatitis B da C), da na ƙwayar cuta mai karya garkuwar jiki wato (HIV).

Gwamna Abba Kabir ya sanya hannu kan dokar ne, bayan kwashe mako guda da majalisar dokokin jihar ta amince da ita.

Sannan kuma dokar ta haramta tsangwamar mutane masu fama da cuta mai karya garkuwar jikin ɗan adam wato HIV, ko kuma cutar amosanin Jini Sikila, ko cutar Hanta, da sauran su.

Har ila yau, sanarwar ta ce dokar za ta fara aiki ne, daga ranar 13 ga watan Mayu na shekarar 2024 da ake ciki.

Continue Reading

Manyan Labarai

Lauya ya nemi a biya Abduljabbar Kabara Naira miliyan 20 saboda ɓata masa lokaci da aka yi.

Published

on

Babbar kotun jaha a ɓangaren ɗaukaka ƙara ƙarƙashin masu Shari’a Aisha Mahamud, da Nasir Saminu, sun sanya ranar 9 ga wannan watan da ake ciki dan ci gaba da sauraron daukaka karar, da Abduljabbar Nasir Kabara ya shigar.

A zaman kotun na yau lauyan Abduljabbar, Barrista Yusuf Sadik, ya shaidawa kotun cewar a shirye suke a fara sauraron daukaka karar.

Sai dai lauyan gwamnati ya bayyana cewar basu shirya ba dan haka a sanya wata ranar.

Lauyan Abduljabbar ya shaidawa kotun cewar sun bai wa lauyoyin gwamnati takardun bayaninsu tun a watan 2 da ya gabata, dan haka a biya Abduljabbarun Naira miliyan 20 saboda ɓata masa lokaci da aka yi.

Sai dai lauyan gwamnati ya yi suka an kuma duba lokacin da aka bada takardun a watan uku ne dan haka wannan lauya ya janye rokonsa.

Daga nan ne kotun ta sanya ranar 9 ga watan nan na Mayu da ake ciki, an kuma umarci lauyan gwamnati da ya yi martani idan yana da shi kafin wannnan rana.

Wakilinmu na Kotu Yusuf Nadabo Isma’il ya rawaito cewa, Abduljabbar Nasir Kabara dai ya daukaka karar ne dan kalubalantar hukuncin kutun shari’ar muslunci ta kofar kudu, wadda ta yanke masa hukuncin kisa ta hanya rataya bisa samunsa da laifin ɓatanci.

Continue Reading

Manyan Labarai

Gobara ta ƙone tarin kayayyaki a gidan tsohon gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau

Published

on

Wata Gobara ta tashi a Gidan Tsohon Gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau dake Mudubawa a yankin Karamar hukumar Nassarawa, inda ta ƙone wasu kayayyaki a ɗakin matar sa waɗanda zuwa yanzu ba’a ƙayyade ba.

Rahotanni sun bayyana cewa gobarar ta faro ne daga ɗakin Girki na matar tsohon gwamnan Hajiya Halima Shekarau, tun yammacin jiya Lahadi.

Da yake tabbatar da faruwar al’amarin, mai magana da yawun tsohon Gwamnan Malam Sule Ya’u Sule, ya ce gobarar ta shafi iya daki ɗaya ne a cikin gidan dake Munduɓawa.

A nasa ɓangaren kakakin hukumar kashe gobara ta jihar Kano, PFS Saminu Yusuf Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce da zarar sun kammala tattara alƙaluma da bincike, zai magantu a nan gaba.

Continue Reading

Trending