Connect with us

Labarai

Mu rinka tuna ranar haduwar mu da ubangijin mu –Ibrahim Tofa

Published

on

Limamin masallacin juma’a na Masjid Quba dake unguwar Tukuntawa a karamar hukumar birni a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abubakar Tofa, ya ce al’ummar musulmai su yi kokari su rinka tuna irin kwanaki biyar da suke a gaban mutum tun kafin komawar sa zuwa wurin mahaliccin sa.

Mallam Abubakar Tofa, na wannan jawabin ne ta cikin hudubar sallar juma’a da ya gabatar a masallacin yau dinnan.

Ya ce” Kwanaki biyar da muke tunatar da kawunan mu, ranar da za ta zo da wadda ta wuce da ranar da muke ciki da wadda za ta zo da kuma ranar busa da kuma ranar ta tashin al-kiyama, mu yi kokari mu yi mafani abubuwa biyar da al’kurani.”

Limamanin ya kuma ce” Mu yi amfani da abu buw biyar kafin biyar su zo, sakamakon samarin mu a yanzu sun shantake, sabida samarin mu a yanzu sun shagala, kuma samarin mu su ne abin tausayi irin abubuwan shagalta da a ka kawo mana ga kuma shaye-shaye da ya addabi samarin namu”. Inji Mallam Ibrahim.

Da yake rufe jawabin sa limamin ta bakin wakilin mu Ibfrahim Abdullahi Sorondinki ya kara da cewar”Ranar gobe kiyama za a yi maka tambaya hudu tambayar nan ta na cikin samartaka idan saurayi ya dace zai zama dan inuwar al’arshi a ranar da babu inuwa, mafita kawai ita ce abun da Allah ya gaya mana kamar yadda ya fada a gobe kiyama zai yi tambaya, kamata ya yi a ce kullum mutum zai yi sallah sau (17) a rana a kalla kennan in ba ka nafila”. A cewar limamin masallacin juma’a na Quba dake Tukuntawa, Mallam Ibrahim Abubakar Tofa.

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending