Manyan Labarai
Hukumar Hisba ta tarwatsa gidan wata kawaliya.

Hukumar Hisba ta jihar Kano ta yi nasarar tarwatsa gidan wata mata da ake zargin ta na kawalcin maza da mata a unguwar Danbare, inda aka yi zargin wasu ‘yan matan na tarewa a gidan suna aikata Badala.
Daga cikin wadanda ake zargin sun tare a gidan har da wata matashiya Hadiza wacce ta bar gidan iyayenta su ke ta neman ta.
Daga bisani dai iyayen nata su ka je hukumar ta Hisba domin ta nemo ma ta ‘yar ta su, inda hukumar ta baza jami’anta suna bin gidajen da ake zarginsu da aikata badala, bincikensu kuma ya gano cewar ta na gidan matar da ake zarginta da yin kawalci, su ka kamo ta da sauran wasu matan har dama ita matar da ake zargin, kuma da zuwan su hukumar aka fara yi musu gwajin cutar HIV.
Wakilinmu Ibrahim Abdullahi Soron Dinki ya zanta da wani daga cikin ‘yan’uwan samarin da aka kama a gidan inda ya ce, “Wannan ita ce take jan su, saboda kamar yadda aka fada wannan tsohuwa kowa ya na ganinta za ta je ta samu yaran (may be) kila cikin iya magana, kuma wannan yaro sana’arsa ma kafinta ya na taimakawa iyayensa, musamman ma mahaifiyarsa, idan aka je aka gaya ma ta za ta ce ba halinsa ba ne.
Matasan da aka kama a gidan sun nuna nadamar su, kuma su ka ce wannan shi ne karo na karshe ba za su kuma aikatawa ba.
Sai dai wacce ake zargin, ta ce ba za ta yi magana a rediyo ba, inda ta kuma bada hanzarinta da cewar, ita ba kawaliya ba ce kasuwanci ta ke a wannan gida.
Mataimakin Babban Kwamandan hisbar kan al’amuran yau da kullum wanda Malam Tasi’u Ishak ya ce, “Babu shakka duk inda kaga tsohon banza to asali yaron banza ne, saboda haka idan aka samu irin wannan, matakin da za’a dauka shi ne mataki na hukuma, ta yadda za a kai ga alkali, shi kuma alkali ya yi hukuncin da ya dace.”
Ya kuma kara da cewar, “Duk sanda namiji ko mace ya dauki harkar fasikanci sana’a, to ya na kan fadawa cikin garari, saboda haka tabbacin akwai cutar ko babu sai (result) sakamako ya fito, daga nan ne mutum zai san babu, kuma ko mutum yaga babu bai hana anjima ya kamu da cutar ba idan ya ci gaba da yi.”
Wakilin namu ya so jin ta bakin ‘yan matan suma amma sai su ka ki cewa komai.

Manyan Labarai
Fadan dabar kofar Na’isa da kofar Dan-agundi, laifin iyaye – Mazaunin Yankin

Wani mazaunin ƙofar Na’isa wanda ya buƙaci a sakaye sunansa, ya ce faɗan dabar da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a yankin da Ɗan Agundi, laifin iyaye ne, da kuma wasu manya a unguwannin da ake zargin suna goya musu baya ta hanyar daƙile yunƙurin hukumomi na ɗaukar doka a kansu.
Mutumin ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, biyo bayan yadda rikicin faɗan dabar ya sake ɓarkewa a unguwannin a Alhamis ɗin nan, al’amarin da ya janyo asarar dukiyoyin al’umma a yankunan.
Ya ce lamarin ya faro ne tun a lokacin bikin ƙaramar Sallah, lamarin da a baya ƙura ta lafa, sai dai kuma a ranar Alhamis ɗin sai gashi an sake samun faɗan dabar.
A cewar sa, “A lokacin faɗan dabar ya faru an Sassari mutane da dama, hatta Saniya ma ba ta tsira ba sai da aka sareta, tare da fasa gilasan ababen hawan Mutane, “in ji shi”.
Sa dai mutumin ya ce, tuni jami’an tsaron Ƴan Sanda, suka kai ɗauki tare da kwantar da tarzoma, lamarin da ƙurar ta lafa.

Manyan Labarai
Ba za mu amince da yadda ake yawan kai wa jami’an mu hari ba a Kano – KAROTA

Hukumar kula da zirgar-zirgar ababen Hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta ce ba za ta lamunta da yadda ake yawan kai wa jami’anta farmaki ba, na ba gaira babu dalili yayin da suke gudanar da ayyukan su.
Shugaban Hukumar KAROTA, a Kano, Injiniya Faisal Mahmud Kabir, ne ya yi wannan gargaɗin ta cikin sanarwar da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya aikowa tashar Dala FM Kano, a ranar Laraba 09 ga watan Afrilun 2025.
“Hakan na zuwa ne biyo bayan wani mummunan hari da wasu mutane da ke cikin baburin Adai-daita sahu suka kai wa jami’an na mu yayin da suke tsaka da aikinsu a titin da ke dab da gidan Buhari kan hanyar zuwa Gidan Zoo, “in ji shi“.
Sanarwar ta ce, tunda farko an tsayar da wani mai baburin Adai-daita Sahu ne inda yaƙi tsayawa, sai kawai aka hango mai ɗan sahun ya naushi jami’in karotar.
Sai dai a ta bakin Shugaban kungiyar ‘Yan Adai-daita Sahu a jihar Kano, ya ce waɗannan mutane ba halattattun ‘Yan Adai-daita Sahu ba ne, sun dai fake da sana’ar su dan aikata ta’addanci.
Daga bisani dai jami’n hulɗa da jama’a na Hukumar Koratar, Abubakar Ibrahim Sharada, ya ce hukumar za ta ɗauki tsattsauran mataki akan lamarin, don kare afkuwar irin hakan a gaba.
Hukumar ta ce duk wanda ya ga faruwar wani abu da ya shafe ta, ko kuma ƙorafe-ƙorafe, zai iya kiran waɗannan lambobin domin sanar da ita, da suka haɗar da 09015709449 ko 08059689422 ko kuma 08067311520.

Manyan Labarai
Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.
Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a
“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.
Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.
Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su