Connect with us

Manyan Labarai

Hukumar Hisba ta tarwatsa gidan wata kawaliya.

Published

on

Hukumar Hisba ta jihar Kano ta yi nasarar tarwatsa gidan wata mata da ake zargin ta na kawalcin maza da mata a unguwar Danbare, inda aka yi zargin wasu ‘yan matan na tarewa a gidan suna aikata Badala.

Daga cikin wadanda ake zargin sun tare a gidan har da wata matashiya Hadiza wacce ta bar gidan iyayenta su ke ta neman ta.

Daga bisani dai iyayen nata su ka je hukumar ta Hisba domin ta nemo ma ta ‘yar ta su, inda hukumar ta baza jami’anta suna bin gidajen da ake zarginsu da aikata badala, bincikensu kuma ya gano cewar ta na gidan matar da ake zarginta da yin kawalci, su ka kamo ta da sauran wasu matan har dama ita matar da ake zargin, kuma da zuwan su hukumar aka fara yi musu gwajin cutar HIV.

Wakilinmu Ibrahim Abdullahi Soron Dinki ya zanta da wani daga cikin ‘yan’uwan samarin da aka kama a gidan inda ya ce, “Wannan ita ce take jan su, saboda kamar yadda aka fada wannan tsohuwa kowa ya na ganinta za ta je ta samu yaran (may be) kila cikin iya magana, kuma wannan yaro sana’arsa ma kafinta ya na taimakawa iyayensa, musamman ma mahaifiyarsa, idan aka je aka gaya ma ta za ta ce ba halinsa ba ne.

Matasan da aka kama a gidan sun nuna nadamar su, kuma su ka ce wannan shi ne karo na karshe ba za su kuma aikatawa ba.

Sai dai wacce ake zargin, ta ce ba za ta yi magana a rediyo ba, inda ta kuma bada hanzarinta da cewar, ita ba kawaliya ba ce kasuwanci ta ke a wannan gida.

Mataimakin Babban Kwamandan hisbar kan al’amuran yau da kullum wanda Malam Tasi’u Ishak ya ce, “Babu shakka duk inda kaga tsohon banza to asali yaron banza ne, saboda haka idan aka samu irin wannan, matakin da za’a dauka shi ne mataki na hukuma, ta yadda za a kai ga alkali, shi kuma alkali ya yi hukuncin da ya dace.”

Ya kuma kara da cewar, “Duk sanda namiji ko mace ya dauki harkar fasikanci sana’a, to ya na kan fadawa cikin garari, saboda haka tabbacin akwai cutar ko babu sai (result) sakamako ya fito, daga nan ne mutum zai san babu, kuma ko mutum yaga babu bai hana anjima ya kamu da cutar ba idan ya ci gaba da yi.”

Wakilin namu ya so jin ta bakin ‘yan matan suma amma sai su ka ki cewa komai.

Manyan Labarai

Zamu ƙone duk kayayyaki marasa inganci da muka kama da zarar an gama shari’u – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta ƙone dukkanin kayayyaki marasa inganci da ta kama, da zarar an kammala dukkanin shari’un da suke a gaban Kotu.

Kwamishinan ma’aikatar ciniki da masana’antu, Adamu Aliyu Kibiya, ne ya tabbatar da hakan, a yayin wata ziyara ta musamman da ya kai hukumar kula da ingancin kayayyaki ta jihar Kano, a yammacin yau Alhamis.

Amadadin Kwamishinan babban sakataren ma’aikatar, Muhammad Yusuf Ɗan-duwa, ya ce, da zarar an kammala Shari’un da masu kayan za’a ƙone su baki ɗaya.

“A bisa al’adar ma’aikatar ciniki da masana’antu, dama duk sabon Kwamishina idan ya zo yana ziyarartar hukumomin da suke da jiɓi da ma’aikatar domin duba irin aikace-aikacen su da sauran abinda ba’a rasa ba, hakan ya sa ma Kwamishinan ya ziyarci hukumar a yau, “in ji Ɗan-duwa”.

 

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, babban sakataren ya ƙara da cewa, ziyarar da Kwamishinan ciniki da masana’antun Alhaji Adamu Aliyu Kibiya, ya kai hukumar kula da ingancin kayayyakin, itace ta farko.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yiwa ma’aikatan ta ci gaban mai haƙan rijiya ne – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Universal Declaration of Human Rights, ta ce ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yiwa ma’aikatan ta, ci gaban mai haƙan rijiya ne, domin ba zai magancewa ma’aikatan matsalolin su ba.

Daraktan ƙungiyar reshen jihar Kano Alhaji Umar Sani Galadanci, ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da wakilinmu na ƴan Zazu Hassan Mamuda Ya’u, a yau Laraba, lokacin da yake tsokaci a kan bikin ranar ma’aikata da ake gudanarwa yau a Najeriya.

Ya kuma ce kasancewar ƙarin albashin ba zai ragewa ma’aikatan wata damuwa ba, sai dai ma ya tunzura ma’aikatan, bai kamata ƙungyoyin ƙwadago su amine da tsirarun ƙarin ba.

“Matukar gwamnatin tarayya za ta rinƙa tunzura ma’aikata da irin wannan tsirarun albashin babu makawa zamu gurfanar da ita a gaban kotu, “in ji Galadanci”.

Umar Sani ya kuma shawarci gwamnatin tarayya da ta lalubo sabbin hanyoyi da za’a ƙarawa ma’aikatan albashi mai tsoka wanda zai rinƙa magance musu wasu matsalolin su na yau da kullum.

Har ila yau, suma ƙungiyoyin ƙwadago a ƙasar nan, sun yi fatali da ƙarin albashin da gwamnatin tarayya ta yiwa ma’aikatan ta da kashi 25 cikin ɗari, da kuma kashi 35 a cikin ɗari.

Ƙungiyoyin ƙwadago da dama na NLC, da TUC, da sauran ƙungiyoyi ne suka gudanar da taron ranar ma’aikan a sassan jahohin ƙasar nan.

Continue Reading

Manyan Labarai

Kayan aikin ginin da ya ruftawa magina a Kuntau ba masu inganci ba ne – Cibiyar masu Taswirar Zane-zanen Muhalli

Published

on

Cibiyar masu tasawirar zane-zanen muhalli ta ƙasa reshen jihar kano, tayi Allah wa dai da kayan da akayi wani ginin Bene da shi mai hawa uku, da ya faɗo akan wasu magina a cikin unguwar Kuntau da ke yankin karamar hukumar Gwale a jihar kano.

Mataimakin shugaban ƙungiyar na kasa Arct Ali Mukhtar, ne ya bayyana hakan a lokacin da cibiyar takai ziyara wajen da al’amarin ya faru.

Ya ce dukkanin kayan da aka yi aikin ginin benen da su ba masu inganci ba ne.

A nasa jawabin shugaban cibiyar a nan nano Arct Bashir Hassan Hanga, kira ya yi ga gwamnatin jihar kano, da ta hana duk masu irin wannan gine-gine ba tare da sahalewar hukumar tsara birane ba wato Knupda, ta kuma ɗauki mataki akan mamallakin wannan gini da ya rushe a kan maginan.

Wakilin mu Shamsu Dau Abdullahi ya rawaito cewa dukkanin tawagar cibiyar tsara gine-ginen, sun ce za su ziyarci asibitin Murtala Muhammad, domin duba mutanen da gini ya fadowa da kuma zuwa ta’aziya gidan waɗanda suka rasu su uku.

Continue Reading

Trending