Connect with us

Manyan Labarai

Karota ta daure ta kara mana lokaci inji direbobin Adaidaita Sahu

Published

on

Laraba 29 ga watan Janairu ita ce ranar karshe kan wa’adin da hukumar Karota ta baiwa direbobin Adaidaita Sahu, na kammala yin sabuwar rijista, ko kuma ta fara kama su a ranar Alhamis 30 ga watan na Janairu.

Tun a jiya Litinin ne dai shugaban hukumar ta karota Baffa Babba Dan Agundi ya ba da wa’adin kwanaki uku ga direbobin Adaidaita Sahun, a yayin wani taro da su ka gudanar da shugabnnin kungiyar ta ‘yan adaidaita sahu.

Ya na mai cewa, “Ranar Laraba in Allah ya yarda ita ce rana ta karshe na yin rijistar  Adaidaita sahu wanda yanzu haka ina tare da shugabannin Adaidaita sahun, kuma daga ranar Larabar idan an rufe ina fatan wanda bai je yayi rijistar ba zai je ya ajiye Babur dinsa. Don haka mu na fata ga wadanda ba su riga sun karasa rijistarsu ba, to su yi kokari su kara sa daga nan zuwa ranar Laraba wadda ita ce ranar karshe.”

To ko a yau da wa’adin ya rage kwana daya, me ne ne ra’ayin direbobin Adaidaita Sahun? Wakilin mu Abubakar Isma’il ya jiyo mana ra’ayoyin wasu direbobin.

“Ni Allah yaba ni ikon yi, sannan ‘yan uwana wadanda basu yi ba Allah ya ba su ikon yi, to amma mu na neman alfarma ga MD na hukumar Karota, wadanda ba su yi ba a daure a kara masu lokaci. In dai gwamnati ta fito da wani tsari ka yi din ina ganin shi ne mafita domin na yi ne saboda gudun wulakanci. Wannan lambar gwamnati ta na yi ne domin ta samu kudin shiga, gaskiya ni ban yi ba, kuma ra’ayina ne ban yi ba, kira na ga hukumar Karota da take cewa, za ta rufe nan da ranar Alhamis ta tuna akwai masu aure, akwai matasa wadanda yawanci haya su ke karba.”

Wasu direbobin Adaidaita Sahu kenan su ke bayyana ra’ayoyinsu akan wa’adin fara kama su da zai kare daga gobe Laraba idan har ba su yi sabuwar rijista.

Manyan Labarai

Fadan dabar kofar Na’isa da kofar Dan-agundi, laifin iyaye – Mazaunin Yankin

Published

on

Wani mazaunin ƙofar Na’isa wanda ya buƙaci a sakaye sunansa, ya ce faɗan dabar da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a yankin da Ɗan Agundi, laifin iyaye ne, da kuma wasu manya a unguwannin da ake zargin suna goya musu baya ta hanyar daƙile yunƙurin hukumomi na ɗaukar doka a kansu.

Mutumin ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, biyo bayan yadda rikicin faɗan dabar ya sake ɓarkewa a unguwannin a Alhamis ɗin nan, al’amarin da ya janyo asarar dukiyoyin al’umma a yankunan.

Ya ce lamarin ya faro ne tun a lokacin bikin ƙaramar Sallah, lamarin da a baya ƙura ta lafa, sai dai kuma a ranar Alhamis ɗin sai gashi an sake samun faɗan dabar.

A cewar sa, “A lokacin faɗan dabar ya faru an Sassari mutane da dama, hatta Saniya ma ba ta tsira ba sai da aka sareta, tare da fasa gilasan ababen hawan Mutane, “in ji shi”.

Sa dai mutumin ya ce, tuni jami’an tsaron Ƴan Sanda, suka kai ɗauki tare da kwantar da tarzoma, lamarin da ƙurar ta lafa.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ba za mu amince da yadda ake yawan kai wa jami’an mu hari ba a Kano – KAROTA

Published

on

Hukumar kula da zirgar-zirgar ababen Hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta ce ba za ta lamunta da yadda ake yawan kai wa jami’anta farmaki ba, na ba gaira babu dalili yayin da suke gudanar da ayyukan su.

Shugaban Hukumar KAROTA, a Kano, Injiniya Faisal Mahmud Kabir, ne ya yi wannan gargaɗin ta cikin sanarwar da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya aikowa tashar Dala FM Kano, a ranar Laraba 09 ga watan Afrilun 2025.

“Hakan na zuwa ne biyo bayan wani mummunan hari da wasu mutane da ke cikin baburin Adai-daita sahu suka kai wa jami’an na mu yayin da suke tsaka da aikinsu a titin da ke dab da gidan Buhari kan hanyar zuwa Gidan Zoo, “in ji shi“.

Sanarwar ta ce, tunda farko an tsayar da wani mai baburin Adai-daita Sahu ne inda yaƙi tsayawa, sai kawai aka hango mai ɗan sahun ya naushi jami’in karotar.

Sai dai a ta bakin Shugaban kungiyar ‘Yan Adai-daita Sahu a jihar Kano, ya ce waɗannan mutane ba halattattun ‘Yan Adai-daita Sahu ba ne, sun dai fake da sana’ar su dan aikata ta’addanci.

Daga bisani dai jami’n hulɗa da jama’a na Hukumar Koratar, Abubakar Ibrahim Sharada, ya ce hukumar za ta ɗauki tsattsauran mataki akan lamarin, don kare afkuwar irin hakan a gaba.

Hukumar ta ce duk wanda ya ga faruwar wani abu da ya shafe ta, ko kuma ƙorafe-ƙorafe, zai iya kiran waɗannan lambobin domin sanar da ita, da suka haɗar da 09015709449 ko 08059689422 ko kuma 08067311520.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Published

on

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.

Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a

“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.

Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.

Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

Continue Reading

Trending