Connect with us

Labarai

Kowa ya dawo da kujerar da ya yi karatu a kanta: WTC Kano

Published

on

Shugabar kungiyar tsofaffin daliban makarantar horas da malamai mata ta WTC wadda ta koma GGC KANO a yanzu Farfesa Fatima Muhammad Umar ta ce kungiyar ta dauki tsarin ne kowaccensu ta dawo da madadin kujerar da tayi karatu akanta lokacin tana daliba da nufin Samar da isassun kujerun Zama a tsohuwar makarantar tasu.

Farfesar ta bayyana hakan ne a lokacin babban taron kungiyar Mai shekaru 73 da kafuwa yau Asabar a harabar makarantar.

Ta Kuma ce da tsarinne na kowa ya dawo da kujerarsa me taken (bring back your chair) yanzu haka suka samu nasarar samarwa da makaranatar Karin kujerun Zama 1380, a hannu guda Kuma suka Samar da rijiyar burtsatse da Kuma gyaran wadanda suka lalace, Baya ga sada zumunci da suke yi a tsakanin su ta dalilin kungiyar.

A nata bangaren tsohuwar daraktar makarantar Dr. Mariya Aliyu Waziri, tace dukda irin gudunmawar da manyan fitattun matan da makarantar ta yaye irinsu matan gwamnoni dama wadanda suka rike ko Kuma suka rike manyan mukamai suke bayarwa wajen bunkasar makarantar, akwai bukatar su ringa Sanya ‘ya’yansu a makarantar maimakon su ringa kaisu manyan makarantun kudi koma kasashen waje, ta yadda makarantar zata ci gaba da Zama a zuciyarsu su Kuma ci gaba da taimaka mata a koda yaushe.

Wakilinmu Ibrahim Abdullahi Sorondinki ya rawaito cewa a taron ya samu halartar wasu dada cikin manyan tsofaffin daliban makarantar irin su Mai dakin gwamnan Kano hajiya Hafsat Abdullahi Umar Ganduje da Kuma Mai dakin gwamnan jihar Jihagawa, harma da sauran tsofaffin dalibai dama sauran masu ruwa da tsaki a bangaren ilimi inda aka gabatar da jawabai daban-daban kan muhimmancin kungiyoyin tsofaffin dalibai na taimakawa gwamnati kan ci gaban ilimi dama Kuma muhimmancin ilimin baki daya musammanma na ‘ya’ya mata.

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending