Connect with us

Labarai

Kowa ya dawo da kujerar da ya yi karatu a kanta: WTC Kano

Published

on

Shugabar kungiyar tsofaffin daliban makarantar horas da malamai mata ta WTC wadda ta koma GGC KANO a yanzu Farfesa Fatima Muhammad Umar ta ce kungiyar ta dauki tsarin ne kowaccensu ta dawo da madadin kujerar da tayi karatu akanta lokacin tana daliba da nufin Samar da isassun kujerun Zama a tsohuwar makarantar tasu.

Farfesar ta bayyana hakan ne a lokacin babban taron kungiyar Mai shekaru 73 da kafuwa yau Asabar a harabar makarantar.

Ta Kuma ce da tsarinne na kowa ya dawo da kujerarsa me taken (bring back your chair) yanzu haka suka samu nasarar samarwa da makaranatar Karin kujerun Zama 1380, a hannu guda Kuma suka Samar da rijiyar burtsatse da Kuma gyaran wadanda suka lalace, Baya ga sada zumunci da suke yi a tsakanin su ta dalilin kungiyar.

A nata bangaren tsohuwar daraktar makarantar Dr. Mariya Aliyu Waziri, tace dukda irin gudunmawar da manyan fitattun matan da makarantar ta yaye irinsu matan gwamnoni dama wadanda suka rike ko Kuma suka rike manyan mukamai suke bayarwa wajen bunkasar makarantar, akwai bukatar su ringa Sanya ‘ya’yansu a makarantar maimakon su ringa kaisu manyan makarantun kudi koma kasashen waje, ta yadda makarantar zata ci gaba da Zama a zuciyarsu su Kuma ci gaba da taimaka mata a koda yaushe.

Wakilinmu Ibrahim Abdullahi Sorondinki ya rawaito cewa a taron ya samu halartar wasu dada cikin manyan tsofaffin daliban makarantar irin su Mai dakin gwamnan Kano hajiya Hafsat Abdullahi Umar Ganduje da Kuma Mai dakin gwamnan jihar Jihagawa, harma da sauran tsofaffin dalibai dama sauran masu ruwa da tsaki a bangaren ilimi inda aka gabatar da jawabai daban-daban kan muhimmancin kungiyoyin tsofaffin dalibai na taimakawa gwamnati kan ci gaban ilimi dama Kuma muhimmancin ilimin baki daya musammanma na ‘ya’ya mata.

Labarai

Mahukunta ku kawo mana ɗauki a masallacin garin mu – Mazauna garin Ɗan-Dalama

Published

on

Al’ummar garin Ɗan-Dalama da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano, sun koka tare da neman ɗaukin mahukunta kan yadda katangar masallacin Juma’a na garin ta lalace, lamarin da hakan ke barazanar faɗuwar katangar.

Shugaban kwamitin masallacin juma’ar na garin Ɗan Dalama, Mallam Muhammad Mai Nama, ne ya magantu kan al’amarin, inda ya kuma yi kira ga al’umma ciki har da Attajirin ɗan kasuwar nan Alhaji Alhassan Aminu Ɗan Tata, da su kawo musu ɗauki domin gyara katangar masallacin na Ɗan Dalama, bisa yadda take neman faɗuwa.

Ya kuma ƙara da cewa ba iya katangar ce ke barazanar faɗuwar ba, haka ma cikin masallacin ba a cewa komai, duk kuwa da ƴan kwamitin sun yi bakin ƙokarin su, amma dai kawo yanzu akwai gyare-gyaren da ya ke buƙata.

Continue Reading

Labarai

Ba za’a iya wadata mutane da Fetur ba idan gwamnati ba ta sa hannu ba – Bashir Ɗan Mallam

Published

on

Yayin da ake ci gaba da fuskantar tsadar man fetur a ƙasar nan, shugaban kungiyar Dillalan Man fetur da Iskar Gas, ta ƙasa Bashir Ahmad Ɗan malam, ya ce koda kuwa matatar Mai ta Dangote za ta yi ƙarfi ka’in da na’in, ba lallai ne a samu saukin Man fetur ba a ƙasa, matuƙar gwamnatin tarayya bata sa hannu ba.

Bashir Ɗan Malam ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da gidan rediyon Dala FM, da safiyar yau Juma’ar.

Ɗan Mallam ya kuma ce sakamakon yadda gwamnati take taimakawa a fagen shan man, hakan yasa idan har bata sanya hannu ba za’a rinƙa shan wahala wajen samun man fetur ɗin a ƙasa.

Wannan dai na zuwa ne yayin da al’umma ke ci gaba da fuskantar ƙalubalen tsadar man fetur, lamarin da ya sa ake siyar da kowacce lita sama da Naira 800 a jihar Kano, inda ake ci gaba da fuskantar manyan layuka a gidajen man da dama.

Continue Reading

Labarai

Zamu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ƴan Jarida – Hukumar Zaɓe ta Kano

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSEC, ta sha alwashin aiki kafaɗa-kafaɗa da ma’aikatan Jarida, musamman ma da zaɓen ƙananan hukumomin jihar nan 44 da ke tafe.

Sabon shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Manumfashi, ne ya bayyana hakan, yayin ziyarar da tawagar ƙuniyar matasan ƴan Jarida, ta Kano Youth Journalist Forum, suka kai masa a ofishin sa yau Alhamis, yayin da ya shafe kwanaki huɗu da kama aiki.

Ya kuma ce, za su yi aiki da ma’aikatan Jarida musamman ma yayin gudanar da ayyukan zaɓen ƙananan hukumomin Kano 44, da ke tafe, domin wayar da kan al’umma da ma samun nasara yayin zaɓen da ma bayan sa.

Farfesa Manumfashi, ya kuma ƙar da cewa, akwai buƙatar kowa ya bayar da tasa gudummawar a harkar zaɓe, domin kuwa yanzu haka suna ci gaba da aiki wajen shirya zaɓen ƙananan hukumomin.

Da yake nasa jawabin shugaban ƙungiyar matasa ƴan Jaridar ta jihar Kano Musa Zangina Adam, ya ce sun kai ziyarar ne, domin su ƙulla alaƙar aiki a tsakanin su da hukumar, bisa yadda kowanne ɓangare yake buƙatar juna, tare kuma da bayar da gudunmawar da ya kamata.

Zangina, ya kuma ce a shirye ƙungiyar su take wajen ci gaba da bibiyar al’amuran da suka shafi al’umma, tare da nusar da mahukunta dan ganin an wadata su da kayayyakin more rayuwa.

Continue Reading

Trending