Connect with us

Manyan Labarai

Zabe: An jefa kuri’a a kan budurwa domin zabar miji

Published

on

Wasu samari biyu sun jefa kuri’ar zabe kato bayan kato, bayan tsawon kwanaki uku ana yin kamfen, akan son wata bakar budurwa, ‘yar Bauchi dake garin Giyade, Hajara Muhammad.

Samarin, Yunusa Muhammad da Ibrahim Adamu, sun kamu ne da kaunar budurwar, wadda itama ta kamu da kaunar tasu, ta kuma umarce su da suje su kada kuri’ar zabe.

Bayan da aka sanar da Dattawan garin, sai aka kuma bude kofar kamfen tsawon kwanaki uku, wanda aka yi zaben karkashin kulawar jami’an tsaron garin, inda itama budurwar ta kai ziyarar gani da ido filin zaben.

Bayan kammala zaben, Yunusa Muhammad, shi ne ya yi nasara, an kuma ba shi tikiti, sakamakon lashe zaben da ya yi, sai dai amma shi wanda bai samu nasara ba, Ibrahim Adamu ya ce, “Bai yarda da zaben ba, tun da dai dama a kofar gidan abokin karawar ta wa a ka yi zaben, domin haka ya zama Inconclusive.”  Inji Ibrahim.

Sai dai bamu samu zantawa da ango mai nasara Yunusa Muhammad ba, amma Aminsa Tajuddin Umar ya bayyana cewa, “Wanda ya fadin, ya rage nasa mu dai mun riga mun yi nasara, har ma mun fara shirye-shiryen fati.”  A cewar aminin ango

Shima Sakataren zaben, Ibrahim Taldo Giyade, ya ce, “Tsakani da Allah mu kai zaben mu, domin dai har da jami’an tsaro ma a wajen, amma dai wanda ya fadin, mun ba shi wa’adin mako guda ya daukaka kara wurin mahukunta.”

Itama amaryar Hajara Muhammad, ta ce, “Koda dai nima ya sanar da ni bai gamsuba, amma dai a wurina zaben ya kammala, saura kuma sai abun da hukumar zaben ta aiwatar.”

Malam Aminu Kidir limamin masallacin Usman Bin Affan dake Kuntau karamar hukumar Gwale, ya yi bayanin matsayin irin wannan aure da  samarin suka yi zasu zaben kuri’a a mahangar addinin musulinci da cewa, “Musulunci ya haramta nema cikin nema, domin haka ba ya halatta wani na neman aure wani kuma ya shigo, sai in wancan ya yi ikirarin ya janye, kuma wannan zaben da suka yi a kan budurwa babu aibu a kansa ko auren a ka yi ya yi, abun da a ke bukata kenan, yayin da samari suka hadu a kan budurwa to su yi kuri’a domin a fitar da mutum daya kwakkwara.” Inji Malam Kidir

Manyan Labarai

Sulhu da ƴan Bindiga ba zai haifar da Ɗa mai ido ba – Human Rights 

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta ƙasa da ƙasa wato International Human Rights Commission, ta ce sulhu da ƴan bindiga ba zai haifar da Ɗa mai ido ba a ƙasar nan.

Babban daraktan ƙungiyar Kyaftin Abdullahi Bakoji Adamu mai ritaya, shi ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM Kano.

Ya ce kasancewar ƴan bindigar basu da wata manufa bai kamata ayi sulhu da su ba, mai-makon hakan yafi dacewa a rinƙa ɗaukar tsauttsauran mataki akan su duba da yadda suke cutar da al’umma.

Ya kuma ce batun da mai bai wa shugaban ƙasa akan sha’anin tsaro Malam Nuhu Ribaɗo, ya yi a baya baya nan, kam cewar an fara samun fashimtar juna da wasu daga cikin ƴan Bindigar da suka addabi mutane a sassan ƙasar nan, a wani ɓangare ma kama da yin sulhu da su, ya faɗi hakan ne kawai amma hakan ba zai haifar da Ɗa mai ido ba.

Continue Reading

Manyan Labarai

Gwamnatin Kano ta kulle wata makaranta mai zaman kan ta a jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta rufe wata makaranta mai suna Golden Crown International School a jihar, da ke yankin Sabon gari, bisa zargin an fake da sunan makarantar ana haɗa magani mara inganci mai-makon koyar da karatu a ciki.

Shugaban kwamitin yaki da miyagun ƙwayoyi da ƙwacen waya na jihar Kano General Gambo Mai Aduwa Mai ritaya, ne ya bayyana hakan, a lokacin da Kwamitin ya kai wani sumame da karfe uku da rabi na daren jiya Talata.

Rahotanni sun bayyana cewa makarantar tana kan titin Zungero da ke cikin ƙaramar hukumar Fagge a jihar Kano, wanda bayan samun bayanan sirri aka ɗauki matakin kulle ta.

Mai Aduwa, ya ƙara da cewar tsarin gurin ta waje ya nuna makaranta ce amma kuma sai ake sarrafa magani da ake zargin ingancin sa da bai kai yadda ya kamata ba, tare da ajiye Allurai da kayan haɗa magani cikin ajujuwan mai-makon ɗalibai.

“Za mu faɗaɗa bincike akan al’amarin dan sanin matakin da za mu ɗauka na gaba, “in ji shi”.

Suma masu gadin gurin da muka zanta da su sun bayana cewar, aikin gadi kawai suke yi amma basu da masaniyar abubuwan dake gudana a cikin makarantar, da ake zargin ana sarrafa magani mara ingani da ajiye shi a muhalin da ake zargin bai yi dai-dai da tsarin doka ba.

Wakilinmu Abba Isah Muhammad ya rawaito cewa shugaban kwamitin ya ce, zai ci gaba da bibiyar guraren dake yin abubuwan da za su kawo koma baya ga harkokin lafiya, da ci gaban jihar Kano, musmman wajen yaƙi da miyagun ƙwayoyi da ƙwacen waya.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ƙaramar hukumar Tofa ta musanta zargin gididdiba burtalai a wasu garuruwan ta uku

Published

on

Ƙaramar hukumar Tofa ta musanta batun gididdiba burtalai a garuruwan Yanoko da Gajida da kuma Dindere, dukka a ƙaramar hukumar da ake zargin an siyarwa Manoma, domin suyi aikin Noma.

Shugaban riƙo na ƙaramar hukumar ta Tofa Abubakar Sulaiman Mai Rogo, ne ya bayyana hakan a daren jiya Laraba, lokacin da yake tsokaci kan koken da Fulani Makiyaya mazauna garuruwan suka yi, kan yadda suka zargi an gididdiba burtalai a yankunan su, an siyarwa wasu Manoma, domin suyi aikin Noma, lamarin da suka ce hakan barazana ce a gare su.

Mai Rogo, ya kuma ce ƙaramar hukumar ba ta da hannu wajen gididdiba burtalai a garuruwan, yana mai cewa ko da kansilolinsa daga zuwan su bai taɓa sanin wanda ya siyar da koda kuwa kunya ɗaya ba a cikin shugabancin sa na ƙaramar hukumar domin ayi Noma, haka shima bai siyar ba.

“Yanzu haka ana kan ɗaukar matakin doka akan waɗanda suka fitar da al’amarin, kasancewar maganar tana wajen ƴan sanda, kuma ana faɗaɗa bincike, “in ji shi”.

A ziyarar gani da Ido, da tashar Dala FM Kano, ta kai wasu daga cikin burtalan da aka yi zargin an siyarwa Manoman, ta iske yadda wasu mutane suke share guraren, kamar yadda suka shaida cewa waɗanda aka siyarwa ne suka basu aikin share wajen.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, wannan na zuwa ne bayan da wasu Fulani Makiyaya mazauna garuruwan suka koka, bisa yadda suka ce an gididdiba burtalai a yankunan su, duk da wani manomi yace har takarda aka bashi bayan an siyar masa, lamarin da ya sa su cikin damuwa bisa yadda hakan ka iya sanyawa su rasa guraren da za su yi kiwon Shanun su.

Continue Reading

Trending