Connect with us

Labarai

Lokutan da za a yi Sallar Idi a masallatan Kano

Published

on

Lokutan Sallar Idi Babba da za a gudanar a safiyar ranar Juma’a a wasu daga cikin masallatan Juma’a dake jihar Kano.

Masallacin Juma’a na Ibadur Rahaman Tudun Yola layin Attahiru Jega, za a yi sallar Idi da karfe 7:45 na safiya a harabar Masallacin dake Tudun Yola GRA layin Farfesa Attahiru Jega.

Masallacin idi na garin ‘Yankusa a karamar hukumar Kumbotso za ayi Sallah da karfe 8: 00 na safiya

Masjid Sahaba Kundila Maiduguri Road Kano, za a yi Sallar Idi karfe 8:15.

Masallacin Juma’a, (JIBWIS) Wailari, filin Makarantar Wailari Special Pprimary School za a yi tayar da Sallah karfe 8:30.

Masallacin Idi na garin Durba dake karamar hukumar Kibiya za ayi Sallah karfe 8:45 a filin Idi na garin Durba.

Masallacin Jumu’a na Uhud Na’ibawa Zaria Road za a yi Sallah da karfe 8:30.

Masallacin Abubakar Sadeeq dake Dantamashe A Zangon Gabas za a yi Sallah da 8:00 a karamar hukumar Ungogo.

Garin Dandalama dake karamar hukumar Dawakin Tofa za agudanar da sallar idi babba a ranar Juma’a da misalin karfe 8 a filin makarantar Primary dake garin Dandalama.

Masallacin Bilal dake Karkasara Tarauni za a yi Sallah da karfe 8:00.

Masallacin Abdullahi bin Umar Shekar Mai Daki karfe 8:15.

Masallacin Juma’a na Mariri dake karamar hukumar Kumbotso za a yi sallah 8:15.

Masallacin Nurul Anwar Kwaciri karfe 8:30.

Masallacin Juma’a na Sabilur Rashad dake Ibrahim Umar Street, Hausawa Zoo Road, Za a tayar da Sallah karfe 7:45 na safiya.

Masallacin Jumma’a na ZHERA dake rukunin gidajen Kundila Zoo Road, Za a tayar da Sallah karfe 8 na safe.

Masallacin Juma’a na Sheikh Ibrahim A Ramadan Tudun Nufawa karfe 8:15.

Masallacin Juma’a na Kanwa Madobi karfe 8:00.

Masallacin Juma’a na Bechi Kumbotso karfe 8:30.

Masallacin Juma’a na garin Kumbotso za a yi sallah karfe 8:30.

Masallacin Juma’a na Mariya Sunusi Dan Tata dake Danladi Na Sidi karfe 8:00.

Masallacin Juma’a na Ansaruldin karfe 8:00.

Masallacin Sheikh Ibrahim Inyas Gadon Kaya 8:15.

Masallacin Juma’a na Izala dake ‘Yan Shana Kumbotso 8:30.

Masallacin Mash Arul Haram dake Sabuwar Gandu a karamar hukumar Kumbots za ayi sallah da karfe 8:00.

Masallacin Jauma’a na Abubakar Sadik dake Gwammaja kan titin Tagwayan gida karkashin Liman, Alkali Halhalatul Khuza’i karfe 8:00.

Masallacin Juma’a na Ado Bayero dake garin Ja’en a karamar hukumar Gwale 8:00.

Masallacin Juma’a na Mallam Abubakar Dan Tsakuwa dake Ja’en Ring Road a karamar hukumar Gwale karfe 8:30.

Labarai

Ƙudurin gyaran dokar gudanarwar Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi ya tsallake karatu na ɗaya a majalisar dokokin Kano

Published

on

Ƙudurin gyaran dokar gudanarwar Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke jihar Kano, ya tsallake karatu na ɗaya a zauren majalisar dokokin jihar.

Ƙudurin ya kai wannan mataki ne yayin zaman majalisar na yau Laraba, ƙarƙashin jagorancin shugaban majalisar Alhaji Jibril Isma’il Falgore, bayan da akawun majalisar Alhaji Bashir Idris Ɗiso, ya gabatar da karatun na ɗaya.

Har ila yau, yayin zaman na yau, majalisar ta buƙaci gwamnatin Injiniya Abba Kabir Yusuf, da ta tallafa wa wasu kanikawa da kafintoci bisa iftila’in gobarar da ta ƙone musu kaya na miliyoyin Naira, tare da asarar rayuka a kan titin Lawan Dambazau.

Majalisar ta buƙaci hakan ne biyo bayan ƙudurin gaggawa da wakilin ƙaramar hukumar Birni da kewaye Alhaji Sarki Aliyu Daneji ya gabatar.

Yayin gabatar da ƙuɗurin, ɗan majalisar ya nemi gwamnatin data tallafa wa waɗanda gobarar ta shafa domin rage musu raɗaɗin iftila’in.

Majalisar ta kuma bukaci gwamnatin da ta ɗaga darajar asibitin garin Gano, zuwa matakin babban asibiti domin ƙara inganta kiwon lafiya a yankin har ma da sauran yankuna, kamar yadda ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Shu’aibu Rabi’u ya buƙata.

Wakilinmu na majalisar Auwal Hassan Fagge, ya ruwaito cewa, a dai zaman na yau Laraba, shi ma ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Ƙaraye, Injiniya Ahmed Ibrahim, ya gabatar da ƙudurin neman gwamnatin Kano ta gina titi a hanyar da ta tashi daga mahaɗar titin zuwa sansanin horas da matasa ƴan hidimar ƙasa, ta bi ta Kurugu da Dederi har zuwa Yammedi duk a yankin ƙaramar hukumar Ƙaraye.

Continue Reading

Labarai

Gwamnan kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya sauya shugaban hukumar tattara haraji na jihar

Published

on

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya amince da naɗin Dakta Zaid Abubakar, a matsayin sabon shugaban hukumar tattara kuɗaɗen haraji ta jihar Kano, da kuma Kasim Ibrahim a matsayin babban daraktan hukumar.

Babban daraktan yaɗa labaran gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar da aka aikowa Dala FM Kano, a daren jiya Laraba.

Sanarwar ta ce, tsohon shugaban hukumar Alhaji Sani Abdulkadir Dambo, an mayar da shi ne a matsayin mai bai wa gwamna shawara na musamman kan harkokin zuba jari, wanda kuma sauye-sauyen za su fara aiki nan take.

Continue Reading

Labarai

Wahalar Fetur: Fadar shugaban ƙasa kiyi wani abu dan mutane su samu sauƙi – Ƙungiyar Nothern Concern Soliderity

Published

on

Yayin da al’umma ke ci gaba da fuskantar wahalar man fetur a ƙasar nan, ƙungiyar da ta damu da abubuwan da suka shafi arewacin ƙasar nan ta Northern Concern Soliderity, ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi abinda ya dace dan ganin mutane sun samu wani sauƙi.

Babban jami’in gudanarwar ƙungiyar, kuma sakataren riƙo na zauren gamayyar kungiyoyin Arewacin Najeriya, Kwamared Saddat Usman Maiyaƙi, ne ya bayyana hakan a zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, lokacin da yake nuna takaici kan irin wahalar da al’ummar ƙasa suke sha wajen shan man Fetur a gidajen man.

Ya ce duba da halin matsin rayuwar da al’umma suka samu kansu a ciki, akwai buƙatar shugabanni da masu ruwa da tsaki su kawo ƙarshen wahalar man Fetur ɗin da aka fama da ita.

Kwamared Saddat Maiyaƙi, ya kuma haƙurƙurtar da al’ummar ƙasar nan kan halin ƙuncin rayuwar da suka samu kai a ciki, inda ya yi fatan komai ya zo karshe cikin ƙanƙanen lokaci.

Continue Reading

Trending