Labarai
Buhari ya sake nada Farfesa Yakubu a matsayin shugaban INEC

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sake gabatar da sunan Farfesa Mahmood Yakubu, a majalisar dokokin kasar, domin sake ci gaba da jagorantar hukumar zabe mai zaman kanta wato INEC a wa’adi na biyu.
Shugaba Buhari ya tabbatar da sake naɗa Farfesa Yakubu ne a cikin wata wasika da ya aika wa shugaban majalisar dattiajai Sanata Ahmed Lawan.
Wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun shugaban, Femi Adesina, ta ce bisa tanadin sashi na 154 (1) na kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 da aka yiwa gyaran fuska, “Ina farin cikin gabatar da Farfesa Mahmood Yakubu ga majalisa domin tabbatar da shi a matsayin Shugaban, Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa (INEC) a karo na biyu kuma wa’adi na karshe.
Farfesa Yakubu shi ya jagoranci babban zaben shekarar 2019, da kuma na gwamnoni da ake gudanarwa lokaci daban da babban zaɓe.
Duk da cewa yawancin zabukan da ya jagoranta sun sha suka daga masu sanya ido daga cikin gida da kuma wajen kasar, kan matsaloli da zargin magudi, amma kuma an yaba masa a zaben gwamnoni da ya jagoranta a baya-baya nan a jihohin Edo inda dan takarar jam’iyyar PDP mai hamayya ya lashe da kuma Ondo da dan takarar jam’iyyar APC ya yi nasara.
A watan Oktoba 2015 ne Shugaba Buhari ya naɗa Farfesa Yakubu a matsayin shugaban hukumar INEC, wanda ya maye gurbin Farfesa Attahiru Jega.

Baba Suda
Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.
Cikakken labarin na Zuwa….

Baba Suda
Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.
Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.
Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

Baba Suda
NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.
Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.
A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.
Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

-
Nishadi6 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su