Connect with us

Ƙasashen Ƙetare

Rasha da Amurka: Putin ya garadi Biden a kan dangantaka

Published

on

Shugaban kasar Russia, Vladimir Putin ya gargadi takwaransa na Amurka, Joe Biden, cewa kakaba sabbin takunkumii kan Ukraine na iya haifar da wargajewar dangantakar da ke a tsakani.

A wata wayar tarho da ya yi da yammacin ranar Alhamis, shugaban na Rasha ya ce, irin wannan takunkumin zai zama “kuskure babba”.

A halin da ake ciki a yanzu, Biden ya shaidawa Putin cewa Amurka da kawayenta za su mayar da martani mai tsauri kan duk wani hari da a ka kaiwa Ukraine.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, wannan kiran da Rasha ta nema, shi ne karo na biyu da su ka yi irin wannan tattaunawa a wannan watan kuma ya dauki kusan sa’a guda.

Wannan dai shi ne wani yunkuri na baya-bayan nan na kwantar da tarzoma a kan iyakar Gabashin Ukraine da Rasha, inda jami’an Ukraine su ka ce an aike da sojojin Rasha fiye da 100,000.

Wannan ci gaban ya haifar da damuwa a kasashen Yammacin duniya, inda Amurka ta yi wa Putin barazanar kakabawa Putin takunkumi “kamar wanda bai taba gani ba” mudin idan Ukraine ta fuskanci hari.

Sai dai Rasha ta musanta cewa ta na shirin mamaye kasar, kuma ta ce sojojin na can ne domin yin atisaye, kuma ta ce ta na da damar motsa sojojinta cikin walwala a kasarta.

Duk da cewa bangarorin biyu sun yi musayar kashedi a yayin ganawar, mai ba da shawara kan harkokin wajen Rasha, Yuri Ushakov, ya shaida wa manema labarai jim kadan bayan ganawar Mr Putin ya ji dadin tattaunawar. Ya kara da cewa, hakan ya haifar da “ dankwan alaka mai kyau” domin tattaunawa a nan gaba.
Wani babban jami’in Amurka, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce ganawar ta su ya kasance mai mahimmanci kuma mai ma’ana.

“Shugaba Biden ya sake nanata cewa, gagarumin ci gaba a cikin wadannan tattaunawa na iya faruwa ne kawai a cikin yanayi na tabarbarewar,” in ji Sakatariyar yada labaran Fadar White House Jen Psaki.
Ta kara da cewa “Ya bayyana karara cewa, Amurka da kawayenta da abokan huldarta za su mayar da martani mai tsauri idan Rasha ta kara mamaye Ukraine.”

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji Sun yi juyin Mulki a Gabon

Published

on

Sojoji sun bayyana a gidan talabijin na kasar Gabon tare da sanar da karbi mulki.

Sun ce sun soke sakamakon zaben da ka gudanar ranar Asabar, inda aka ayyana shugaba Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben.

Hukumar zaben ta ce Mr Bongo ya samu nasara ne da kasa da kashi biyu bisa uku na kuri’un da aka kada a zaben da ‘yan adawa suka ce an tafka magudi.

Sun Kuma ce Hambarar da shi zai kawo karshen mulkin shekaru 53 da iyalan gidansu ke yi a Gabon.

Sojoji 12 ne suka bayyana a gidan talabijin dake sanar da soke sakamakon zaben tare da rusa dukkan hukumomin kasar.

Daya daga cikin sojojin ya fada a tashar talabijin ta Gabon 24 cewa, “Mun yanke shawarar kare zaman lafiya ta hanyar kawo karshen mulkin da ake yi a yanzu.”

Mr Bongo ya hau karagar mulki lokacin da mahaifinsa Omar ya rasu a shekara ta 2009.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji sunyi juyin Mulki a jamhuriyar Nijar

Published

on

Rahotanni daga jamhuriyar Nijar na cewa Sojojin Kasar sun yi juyin Mulki, tare da sanar da kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum.

Cikin sanarwar da suka bayar a gidan telebijin din Kasar, jagoran tawagar sojojin Kanal Amadu Abdramane yace “mun kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum tare da karbe dukkanin Wani Iko”.

Sojojin dai sun bayar da dalilin halin rashin tabbas da Kuma Matsin tattalin arziki a kasar.

Tuni dai sojojin suka garkame dukkanin iyakokin Kasar tare da Sanya dokar takaita zirga zirga daga karfe 10 na dare zuwa 6 na safe.

Tun a safiyar laraba ne dai aka wayi gari da fara wancan yunkuri, Wanda yanzu haka ta tabbata, Kasar Nijar na hannun sojoji, Wanda shi ne Karo na hudu ana gudanar da juyin mulkin a jamhuriyar Nijar.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

An tsaurara tsaro a fadar shugaban Kasar Nijar

Published

on

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar, na nuni da cewa dakarun da ke gadin fadar shugaban ƙasa sun rufe duk wata hanyar shiga fadar a wani lamari da ba a kai ga ganowa ba.

Sai dai rahotanni na cewa yanzu haka wasu daga cikin tsofaffin shugabannin ƙasar ta Nijar na tattaunawa da sojojin domin sasanta lamarin.

Karin bayani nan tafe….

Continue Reading

Trending