Connect with us

Ƙasashen Ƙetare

Saudiyya ta sanar da Litinin a matsayin ranar Sallar Idi ƙarama

Published

on

Kasar Saudiyya ta ce, ranar Litinin 2 ga watan Mayu a matsayin ranar Eid-el Fitr saboda ba a ga watan Shawwal ba.

Sanarwar ta ce, ba a iya ganin jinjirin watan Shawwal ba daga dakin kallo na Tamir ko kuma na jami’ar Majmaah da ke Hautat Sudair a ranar Asabar.

A cewar jaridar Saudi Gazette, hakan na nufin ranar Lahadi 1 ga watan Mayu, ita ce ranar karshe ta watan Ramadan, kuma ranar Litinin 2 ga watan Mayu, ita ce ranar farko ta Idin sallah ƙarama ta Al-Fitr.

Ƙasashen Ƙetare

Shek Shuraim yayi ritaya daga limancin Masallacin harami

Published

on

Shek Shuraim

Guda cikin manyan limaman masallaci Mai alfarma na Makkah Shek Shuraim ya rubuta takardar ajiye limancin masallacin.

Shafin Haramain Sharifain ya ruwaito cewa, cikin takarar ajiye limancin da Shek Shuraim ya rubuta, ya bayar da uzurin mayar da hankali kan wasu ayyuka da suka kulla yarjejeniya da shugabancin Kasar tun a shekarar bara ta 2022.

Sai dai takardar ta bayyana cewa, Shek Shuraim zai rinka zuwa masallacin domin jagorantar wasu salloli, musamman Tarawih a watan Ramadhana.

Shek Shuraim dai ya dauki tsawon shekaru Yana Jan sallah a masallacin harami, Kuma guda ne cikin gwanayen alqur’ani, inda wasu lokutan suke karanta shi da Shek Abdurrahman Assudais.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

Yadda birnin Makkah ya koma bayan saukar ruwan sama

Published

on

Kaaba

 

. Yawan korayen ciyayi a birnin Makkah alama ce ta tashin alqiyama.

. Saukar ruwan sama ya sanya korayen ciyayi sun fito a birnin Makkah.

Shafin Haramain Sharifain ya wallafa cewa yanzu haka korayen ciyayi sun mamaye birnin Makkah sakamakon mamakon ruwan sama da aka yi.

Sai dai Malamai irin su Dakta Zakir Naik sunyi fashin baki, Ina suka ce hakan wata alama ce da take nuna kusantowar tashin alqiyama, dogaro da hadisin Annabi S.A.W,

Alqiyama ba za ta tsaya ba har sai yankin larabawa ya koma kiwo da koramu, wanda hakan zai faru ne ta sanadin korayen ciyayi”.  Muslim 157

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

‘Yan Sanda sun ce Beraye ne suka shanye hodar Ibilis a ofishin su

Published

on

‘Yan sandan kasar Indiya, sun ce ɓeraye sun lalata kusan kilogram 200 na hodar Ibilis da aka ƙwace a hannun wasu mutane da ke safararta aka kuma ajiye a ofishinsu.

“Ɓeraye kananan halittu ne da ba su san wani tsoron ‘yan sanda ba. Abu ne mai wahala iya kare su,” a cewar Kotu da ke zamanta a jihar Uttar Pradesh.

Kotun ta bukaci ‘yan sanda su gabatar da shaida da ke tabbatar da cewa ɓeraye ne suka lalata hodar.



Alkalin ya bada misali da kararraki uku da aka gabatar kan ɓeraye sun lalata kwayar.

Mai shari’a Sanjay Chaudhary ya ce ko a baya an samu rahotanni da ke cewa ɓerayen sun lalata kilo 195 na hodar iblis, da kuma kilo 700 duk a ofisoshin ‘yan sanda.

Sanjay ya faɗawa ‘yan sanda cewa ba su da kwarewar yaƙi da irin waɗannan ɓeraye. Ya ce hanya ɗaya tilo na kare aukuwar irin wannan shi ne kai hodar ko kwayar dakunan adana magunguna ko aiwatar da gwaji. In ji BBC.




Continue Reading

Trending