Connect with us

Ƙasashen Ƙetare

Da Duminsa: Maniyaciyyar jihar Nasarawa ta rasu a kasar Saudiyya

Published

on

Maniyaciyar jihar Nasarawa mai suna, Hajiya Aisha Ahmad, ta rasu a yau Laraba sakamakon rashin lafiya a kasar Saudiyya.

Aisha Ahmed ‘yar karamar hukumar Keffi a jihar Nasarawa ta rasu ne bayan ta yi fama da gajeruwar rashin lafiya kamar yadda babban sakataren hukumar jin dadin alhazai ta jihar Nasarawa Idris Al-makura ya tabbatar.

Al-Makura ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na kasa ranar Laraba a birnin Makkah na kasar Saudiyya cewa, Aisha ba ta da wani labari na rashin lafiya kafin ta tashi daga Najeriya.

Ya ce “An fara kai ta Asibitin Hukumar Alhazai ta kasa da ke Makkah, sannan aka kai ta Asibitin Sarki Abdulaziz inda ta rasu. An sanar da iyali yadda ya kamata.

Ya kuma ce, “Mun aika wa dangin ta faifan bidiyo na tsarin tabbatar da mutuwarta, zuwa ga jana’izar ta, kuma a karshe mun yi jana’izar ta,” in ji shi.

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji Sun yi juyin Mulki a Gabon

Published

on

Sojoji sun bayyana a gidan talabijin na kasar Gabon tare da sanar da karbi mulki.

Sun ce sun soke sakamakon zaben da ka gudanar ranar Asabar, inda aka ayyana shugaba Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben.

Hukumar zaben ta ce Mr Bongo ya samu nasara ne da kasa da kashi biyu bisa uku na kuri’un da aka kada a zaben da ‘yan adawa suka ce an tafka magudi.

Sun Kuma ce Hambarar da shi zai kawo karshen mulkin shekaru 53 da iyalan gidansu ke yi a Gabon.

Sojoji 12 ne suka bayyana a gidan talabijin dake sanar da soke sakamakon zaben tare da rusa dukkan hukumomin kasar.

Daya daga cikin sojojin ya fada a tashar talabijin ta Gabon 24 cewa, “Mun yanke shawarar kare zaman lafiya ta hanyar kawo karshen mulkin da ake yi a yanzu.”

Mr Bongo ya hau karagar mulki lokacin da mahaifinsa Omar ya rasu a shekara ta 2009.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji sunyi juyin Mulki a jamhuriyar Nijar

Published

on

Rahotanni daga jamhuriyar Nijar na cewa Sojojin Kasar sun yi juyin Mulki, tare da sanar da kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum.

Cikin sanarwar da suka bayar a gidan telebijin din Kasar, jagoran tawagar sojojin Kanal Amadu Abdramane yace “mun kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum tare da karbe dukkanin Wani Iko”.

Sojojin dai sun bayar da dalilin halin rashin tabbas da Kuma Matsin tattalin arziki a kasar.

Tuni dai sojojin suka garkame dukkanin iyakokin Kasar tare da Sanya dokar takaita zirga zirga daga karfe 10 na dare zuwa 6 na safe.

Tun a safiyar laraba ne dai aka wayi gari da fara wancan yunkuri, Wanda yanzu haka ta tabbata, Kasar Nijar na hannun sojoji, Wanda shi ne Karo na hudu ana gudanar da juyin mulkin a jamhuriyar Nijar.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

An tsaurara tsaro a fadar shugaban Kasar Nijar

Published

on

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar, na nuni da cewa dakarun da ke gadin fadar shugaban ƙasa sun rufe duk wata hanyar shiga fadar a wani lamari da ba a kai ga ganowa ba.

Sai dai rahotanni na cewa yanzu haka wasu daga cikin tsofaffin shugabannin ƙasar ta Nijar na tattaunawa da sojojin domin sasanta lamarin.

Karin bayani nan tafe….

Continue Reading

Trending