Connect with us

Labarai

Mun samu rashin fitowar jama’a wajen yin rijistar katin zabe a Katsina – INEC

Published

on

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta bayyana damuwarta kan yadda mazauna yankin jihar  Katsina suka yi rijistar katin zabe na dindindin (PVC) a sabbin rumfunan zabe 1,750 da aka kafa a jihar.

Alhaji Jibril Zarewa, kwamishinan zabe na INEC a jihar, ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na kasa NAN a ranar Juma’a a Katsina.

Ya ce, bayan shekara daya da fara rajistar PVC, an samu rashin fitowar jama’a domin yin rajista a sabbin rumfunan zabe da aka kafa.

A cewar Zarewa, “A watan Mayun 2022 da muka yi bincike, mun gano a cikin sabbin rumfunan zabe 1,750 da aka kafa, kusan guda 1,200 ba su da mutane sama da 50 da suka yi rajista a kowannen su.

“Wannan rijistar ta ƙunshi canja wuri. Wasu rumfunan zabe ba su da rijista, yayin da wasu ba su wuce mutane 50 da suka yi rajista ba.

“Ko da yake ana iya danganta hakan da dakatar da hanyoyin sadarwa a kananan hukumomi 17 daga cikin 34 na kananan hukumomi kusan watanni biyar saboda matsalar tsaro.

“Muna kira ga al’ummar yankunan da aka kirkiro sabbin rumfunan zabe da su je su yi rajista, domin INEC a shirye take a kodayaushe.

Ya bayyana cewa da farko akwai rumfunan zabe 4,902 a jihar amma tare da samar da karin rumfunan zabe 6,652 a halin yanzu.

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Labarai

Real Madrid ta kaddamar da Alexander

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta ƙaddamar da ɗan wasa Trent Alexander Arnold a yau a matsayin ɗan wasan ta

Inda shugaban ƙungiyar Flerontino Perez yace yau suna matuƙar Farin ciki kasancewar sun mallaki babban ɗan wasan baya a duniya.

 

Shima ɗan Wasa Arnold ya bayyana cewa yana cikin farin ciki kuma mafarkin sa ya cika na zama ɗan Wasan Madrid a yau.

Continue Reading

Daurin Boye

Zan shiga kawancen ‘yan jamiyyar hamayya – tsohon Minista

Published

on

Tsohon ministan sufurin Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce a shirye yake don shiga ƙawancen ƴan jamiyyar hamayya domin ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027

A wata hira da BBC, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce suna ƙoƙarin samar da haɗakar siyasar da za ta samar da sauyi a ƙasar.

Amaechi wanda ɗan jam’iyyar APC ne  ya nuna damuwa kan abin da ya ƙira halin ƙuncin rayuwa da ƙasar ke ciki.

Amaechi ya ce bai cire tsammanin yin takarar shugaban ƙasa ba, illa lokaci ne kawai zai tantance.

Continue Reading

Trending