Labarai
Mun samu rashin fitowar jama’a wajen yin rijistar katin zabe a Katsina – INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta bayyana damuwarta kan yadda mazauna yankin jihar Katsina suka yi rijistar katin zabe na dindindin (PVC) a sabbin rumfunan zabe 1,750 da aka kafa a jihar.
Alhaji Jibril Zarewa, kwamishinan zabe na INEC a jihar, ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na kasa NAN a ranar Juma’a a Katsina.
Ya ce, bayan shekara daya da fara rajistar PVC, an samu rashin fitowar jama’a domin yin rajista a sabbin rumfunan zabe da aka kafa.
A cewar Zarewa, “A watan Mayun 2022 da muka yi bincike, mun gano a cikin sabbin rumfunan zabe 1,750 da aka kafa, kusan guda 1,200 ba su da mutane sama da 50 da suka yi rajista a kowannen su.
“Wannan rijistar ta ƙunshi canja wuri. Wasu rumfunan zabe ba su da rijista, yayin da wasu ba su wuce mutane 50 da suka yi rajista ba.
“Ko da yake ana iya danganta hakan da dakatar da hanyoyin sadarwa a kananan hukumomi 17 daga cikin 34 na kananan hukumomi kusan watanni biyar saboda matsalar tsaro.
“Muna kira ga al’ummar yankunan da aka kirkiro sabbin rumfunan zabe da su je su yi rajista, domin INEC a shirye take a kodayaushe.
Ya bayyana cewa da farko akwai rumfunan zabe 4,902 a jihar amma tare da samar da karin rumfunan zabe 6,652 a halin yanzu.
Labarai
Rahoto: Mu nisanci abinda Allah Ya hana domin samun saukin rayuwa – Limamin Tukuntawa

Limamin masallacin juma’a na Masjidul Kuba da ke unguwar Tukuntawa a jihar Kano, Malam Ahmad Ali, ya ce, al’umma su duba tsakanin su da Allah tare da nisantar abinda ya hana, domin saukin tsadar rayuwa.
Malam Ahmad Ali, ya bayyana hakan ne, yayin da yake yiwa wakilin mu na ‘yan Zazu, Ibrahim Abdullahi Soron Dinki, Karin bayani dangane da abinda hudubar da ya gabatar ta kunsa.
Akwai cikakken bayanin hudubar a muryar da ke kasa.
Labarai
Rahoto: Rubutu na da muhimmanci a mu’amalar bashi – Limamin Bompai

Limamin masallacin juma’a na Shelkwatar rundunar ‘yan sandan jihar Kano da ke unguwar Bompai, SP Abdulkadir Haruna, ya ce, akwai bukatar mu rinka gudanar da mu’amalar bashi yadda addinin musulunci.
SP Abdulkadir Haruna, yana bayyana hakan, a zantawarsa da wakilin mu na ‘yan Zazu, Abba Isah Muhammad, bayar idar da Sallar Juma’a.
Domin jin cikakken rahoton saurari wannan.
Labarai
Rahoto: Matashi ya yi yunkurin cinye tabar Wiwin da aka kama shi da ita a hanyar kotu

Ana zargin wani matashi ya yi yunkurin hadiye tabar Wiwi da miyagun kwayoyi da aka kama shi da ita a hanyar kotu.
Tunda fari jami’an tsaron, sun kama matasahin da zargin samun sa da kayan maye, inda yake boye da wasu basu sani ba, kafin kuma a kai shi kotu, ya ciro su yana yunkurin hadiye wa.
Wakilin mu na ‘yan Zazu, Ibrahim Abdullahi Soron Dinki yana da cikakken rahoton.
-
Nishadi3 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai3 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai2 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Nishadi3 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai2 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Lafiya2 months ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi3 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai3 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano