Connect with us

Ƙasashen Ƙetare

Ban kwanan karshe na Sarauniya Elizabeth ta biyu

Published

on

Shugabannin kasashen duniya sama da dari ciki harda shugaban kasar Amurka Joe Biden da kuma mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbanjo tare da kuma wakilan gwamnati daga kasashe dari biyu ne suka halarci jana’izar Sarauniyar Burtaniya, Elizabeth ta biyu da aka gudanar a birnin Landan a ranar Litinin.

An dai shafe tsawon kwanaki goma sha biyu a na gudanar da bukukuwan mutuwar Sarauniyar da ta shafe shekaru 70 ta na mulki a Burtaniya, daidai lokacin da ta shafe tsawon shekaru 96.

Sama da mutane dubu dari da saba’in ne suka yi jern gwano a bakin fadar Windsor, wurin da za a binne Sarauniya kusa da iyayen ta mijinta Yarima Philips tare da sauran sarakunan da suka shude a yankin Burtaniya.

Bikin jana’aizar dai na mutuwar Sarauniya, shi ne biki mafi girma a Burtaniya sama da shekaru hamsin da suka gabata, za kuma a bar ahalinta su shiga wajen binne ta, yayin da za a dakatar da ‘yan jaridu daga shiga wurin da za a binne ta, kamar yadda ahalin ta suka bukaci hakan.

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji Sun yi juyin Mulki a Gabon

Published

on

Sojoji sun bayyana a gidan talabijin na kasar Gabon tare da sanar da karbi mulki.

Sun ce sun soke sakamakon zaben da ka gudanar ranar Asabar, inda aka ayyana shugaba Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben.

Hukumar zaben ta ce Mr Bongo ya samu nasara ne da kasa da kashi biyu bisa uku na kuri’un da aka kada a zaben da ‘yan adawa suka ce an tafka magudi.

Sun Kuma ce Hambarar da shi zai kawo karshen mulkin shekaru 53 da iyalan gidansu ke yi a Gabon.

Sojoji 12 ne suka bayyana a gidan talabijin dake sanar da soke sakamakon zaben tare da rusa dukkan hukumomin kasar.

Daya daga cikin sojojin ya fada a tashar talabijin ta Gabon 24 cewa, “Mun yanke shawarar kare zaman lafiya ta hanyar kawo karshen mulkin da ake yi a yanzu.”

Mr Bongo ya hau karagar mulki lokacin da mahaifinsa Omar ya rasu a shekara ta 2009.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji sunyi juyin Mulki a jamhuriyar Nijar

Published

on

Rahotanni daga jamhuriyar Nijar na cewa Sojojin Kasar sun yi juyin Mulki, tare da sanar da kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum.

Cikin sanarwar da suka bayar a gidan telebijin din Kasar, jagoran tawagar sojojin Kanal Amadu Abdramane yace “mun kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum tare da karbe dukkanin Wani Iko”.

Sojojin dai sun bayar da dalilin halin rashin tabbas da Kuma Matsin tattalin arziki a kasar.

Tuni dai sojojin suka garkame dukkanin iyakokin Kasar tare da Sanya dokar takaita zirga zirga daga karfe 10 na dare zuwa 6 na safe.

Tun a safiyar laraba ne dai aka wayi gari da fara wancan yunkuri, Wanda yanzu haka ta tabbata, Kasar Nijar na hannun sojoji, Wanda shi ne Karo na hudu ana gudanar da juyin mulkin a jamhuriyar Nijar.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

An tsaurara tsaro a fadar shugaban Kasar Nijar

Published

on

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar, na nuni da cewa dakarun da ke gadin fadar shugaban ƙasa sun rufe duk wata hanyar shiga fadar a wani lamari da ba a kai ga ganowa ba.

Sai dai rahotanni na cewa yanzu haka wasu daga cikin tsofaffin shugabannin ƙasar ta Nijar na tattaunawa da sojojin domin sasanta lamarin.

Karin bayani nan tafe….

Continue Reading

Trending