Connect with us

Wasanni

Arsenal ta gaggauta daukar Ronaldo – Seaman

Published

on

Tsohon mai tsaron ragar Arsenal, David Seaman, ya bukaci kungiyar da ta sayi tsohon dan wasan Manchester United Cristiano Ronaldo.

Seaman ya yi imanin cewa, zai zama cikakkiyar sa hannu idan Arsenal ta kawo Ronaldo filin wasa na Emirates.

Ronaldo a halin yanzu ya na da ‘yanci, bayan da aka soke kwantiraginsa da Manchester United a wannan makon.

An kawo karshen kwantiragin kyaftin din na Portugal kwanaki baya,n wata fitacciyar hirar da ya yi da mai yada labarai Piers Morgan, inda ya caccaki Manchester United, dangin Glazer, Erik ten Hag, da sauransu.

“Ronaldo bai yi nisa ba kuma zai dace da Arsenal,” Seaman ya shaida wa TalkTV.

“Zan yaba masa [ga hirar da ya yi, domin a fili ya na fadin gaskiya. Yawancin kayan da ya fito da su ba kayan da ba mu ji ba.

“Mun ji wasu gogaggun ‘yan wasa da yawa suna nishi da sukar Man United kan yadda kasa take da kuma horo.

“Hakan ya girgiza ni kuma bai kamata hakan ya faru ba. Ya kasance a duk faɗin duniya kuma ya ga yadda ko’ina ya ci gaba kuma ya dawo wurin ƙaunataccen Man United kuma babu abin da ya canza. “

Wasanni

Kungiyar Al-Ittihad ta sallami mai horaswar ta Nuno.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Al-Ittihad da ke kasar Saudiyyah ta sallami mai horaswar ta Nuno Espirito Santo, bayan kwashe watanni 16 ya na horas da ita.

Santo dan asalin kasan Portugal mai shekaru 49, kuma tsohon mai horas da Kungiyar kwallon kafa ta Tottenham Hotspur ta kasar Ingila, ya fara horas da kungiyar Al-Ittihad ne a watan Yuli na shekarar 2022 bayan korar sa da kungiyar kwallon kafa ta Tottenham Hotspur ta yi.

Kungiyar kwallon kafa ta Al-Ittihad dai ta bayyana cewar ta sallami Nuno Espirito Santo ne sakamakon rashin kokari da kungiyar ta ke yi karkashin jagorancin sa, Al-Ittihad dai tayi nasara ne a wasanni 6 cikin wasanni 12 da ta buga a kakar bana.

A ranar Litinin din da ta gabata ne, Kungiyar kwallon kafa ta Air Force ta kasar Iraq, ta doke Al-Ittihad da ci 2 – 0 a wasan zakarun Asian Champions league.

Continue Reading

Wasanni

Kano Pillars ta koma mataki na hudu a gasar NPFL.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta koma mataki na hudu a gasar cin kofin kwararru na Nigerian

Pillar dai ta doke Kungiyar kwallon kafa ta Bayelsa United ne, da ci uku babu ko daya a wasan mako na shida na gasar ta shekarar 2023 zuwa 2024.

A ranar lahadi 5/11/2023 ne kungiyar ta Kano Pillars za ta ziyarci Kungiyar kwallon kafa ta Sporting Lagos a Jihar Lagos a wasan mako na bakwai na gasar.

Continue Reading

Wasanni

Sakamakon wasan mako na hudu na gasar NPFL

Published

on

Sakamakon wasan mako na hudu na gasar cin kofin kwararru na Najeriya na kakar 2023/2024 wato NPFL.

Tun a ranar Asabar din da ta gaba ta ne 21 Oktoba 2023, aka buga wasa daya tilo kamar haka÷

Niger Tornadoes 1 – 0 Bayelsa United

Sai dai an dage wasa tsakanin kungiyar kwallon kafa ta Doma United da Enyimba

Wasanni da aka buga a ranar Lahadi 22 Oktoba 2023 kuwa÷

Gombe United 1 – 0 Bendel Insurance

Akwa United 0 – 0 Shooting Stars

Heartland Owerri 1 – 1 Katsina United

Kano Pillars 1 – 0 Rivers United

Kwara United 1 – 1 Enugu Rangers

Lobi Stars 2 – 0 Abia Warriors

Plateau United 1 – 0 Sunshine Stars

Remo Stars 2 – 1 Sporting Lagos.

Continue Reading

Trending