Rundunar ‘yan sanda jihar Nasarawa, ta ce, ta gano gidan da ake zargin a na sayar da jarirai a karamar hukumar Karu na jihar.
Rundunar ta ce, ta ceto mata shida da kuma jariri ɗan wata shida a gidan.
A sanarwar da suka fitar, jami’in hulda da jama’a na ‘yansanda yankin, DSP Ramhan Nansel, ya ce, da misalin 2 na rana suka kai sumame a Karu, bayan samun wasu bayanan sirri.
Ya ce, “A na basaja da gidan ne a matsayin gidan kula da marayu. Sai dai bincike ya gano cewa, an a garkuwa da kananan yara a na yi musu ciki sannan a sayar da jariran da suka haifa. Mun kuma cafke wasu mutum uku da a ke zargin ke aikata wannan laifin”. In ji DSP Ramhan.