Connect with us

Manta Sabo

Aljanun jikina ne suke sa ni yin Sata – Matar da aka gurfanar a Kotu

Published

on

Kotun majistret mai lamba 54 karkashin jagorancin mai sharia Ibrahim Mansur, ta fara sauraron wata shari’a da ‘yan sanda suka gurfanar da wasu mata biyu wadanda ake tuhuma da laifin hada baki da satar wasu sarkoki da ‘yan kunnaye na daham.

Kunshin tuhumar ya bayyana cewar matan sun hada baki sun shiga wani gida a unguwar sharada, inda akayi zargin sun saci yan kunne da sarka masu kimar Naira Miliyan shida da dubu dari takwas.

Haka kuma ‘yan sandan sun kuma gurfanar da wani matashi wanda ake zargin shine ya sayi sarkar akan kudi Naira dubu dari biyu, inda ya kuma sassara sarkar da yan kunnen dan ya narka su.

Lokacin da aka karanta musu kunshin tuhumar, wadda ake ruhuma ta farko ta amsa laifin sata da hada baki da kuma laifin kutse.

Sai dai wadda ake tuhuma ta biyu ta amsa laifin sata ta kuma musanta ragowar zarge-zargen, yayin da shi kuma Muhammad Abdullahi wanda ake tuhuma na uku ya musanta zargin sayen kayan satar.

Mai gabatar da kara ya roki kotun da ta hukunta wadanda ake tuhumar bisa ikirarin bakinsu.

Kotun ta tambayi matan ko suna da wata hujja da za ta hana a hukunta su, wadda ake tuhuma ta farko ta bayyana cewar wasu aljanu ne a jikinta kuma sune suke sanya ta sata, sai dai kotun bata karbi hanzarinta ba, kotun ta sanya ranar 15 ga wannan wata dan bayyana hukuncinta.

A gefe guda kuma lauyan wanda ake tuhuma na uku ya roki kotun da ta bayar da belinsa, sai dai mai gabatar da kara ya yi suka.

Wakilinmu Yusif Nadabo Isma’il ya rawaito cewa, kotun ta sanya wanda ake tuhuma na uku a hannun beli, idan kuma ya tsere masu karbar belin za su biya Naira miliya 5. wanda shima wanda ake tuhumar zai ajiye Naira miliyan 3.

Manta Sabo

Wata Kotu a Kano ta ci gaba da sauraron ƙarar da aka shigar da ƙaramar hukumar Gwale da wani mutum

Published

on

Babbar kotun jaha mai lamba 15 da ke zamanta a Mila Road a jihar Kano, karkashin jagorancin mai shari’a Sunusi Ado Ma’aji, ta ci gaba da saurarar karar da al’ummar unguwar Dorayi Baba unguwar jakada suka shigar da karamar hukumar Gwale, da wani mutun mai suna Alhaji Ibrahim Ƴan Shana.

Tunda fari dai mutanan unguwar sun shigar da karar ne suna zargin karamar hukumar ta Gwale, da cefanar wa Ibrahim ‘yan Shana wani fili mallakin al’ummar unguwar na makaranta, lamarin da su garzaya gaban kotun tun a shekarar 2023, a lokacin shugabancin ƙaramar hukumar da ya shuɗe, suna rokon da ta dawo musu da shi domin a gida makaranta a yankin nasu.

Sai dai a zaman kotun na yau bangaren wadanda ake kara na daya wato karamar hukumar Gwale sun gaza gabatar da martanin su akan karar, inda suka roki kotun da ta sanya wata ranar domin gabatar da martanin nasu.

Wakilimmu Mu’az Musa Ibrahim ya rawaito cewa mai shari’ar ya sanya ranar 5 ga watan Yunin shekarar 2024 domin ci gaba da shari’ar.

Continue Reading

Manta Sabo

Kotu ta aike da matashin da ake zargi da kashe matar sa gidan yari a Kano

Published

on

Kotun majistret mai lamba 29 karkashin jagorancin mai Shari’a Talatu Makama, ta aike da wani matashi gidan gyaran hali.

Matashin mai suna Adamu Ibrahim ana zargin sa ne da laifin hallaka mai ɗakinsa ta hanyar kwantara mata dutsen Guga, a fuskarta a can garin kwanar ɗan gora.

Ƙunshin tuhumar ya bayyana cewar, tun a ranar 9 ga watan 4, wani mai suna Idris Adamu yaje caji ofishin ƴan sanda inda ya shigar da kara akan cewar Adamu Ibrahim ya kashe mai ɗakinsa wadda kuma kanwa ce a wajen mai ƙarar Idris Adamu.

Bayan fitowa daga kotun ne wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’ila, ya zanta wanda ake zargi wanda ya ce tsautsayinya sanya shi aikata hakan.

Shima dan uwan marigayiyar ya bayyana matsayarsu, inda ya roƙi kotun da ta yi musu adalci a shari’ar.

Kotun dai ta sanya ranar 17 ga watan gobe dan a kara gabatar da shi a gaban ta domin ci gaba da shari’ar.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Trending