Connect with us

Manta Sabo

Kotu ta aike da wata mata gidan Yari kan zargin ta da yanke maƙarfafar mijin ta a Kano  

Published

on

Kotun majistret mai lamba 54 ƙarƙashin jagorancin mai Shari’a Ibrahim Mansur Yola a jihar Kano, ta fara sauraron wata ƙara wadda ƴan sanda suka gurfanar da wata mata mai suna Maryam Imam mazauniyar garin Tofa, inda ake zargin ta da laifin yanke makarfafar mijinta Abubakar Imam.

Yayin da aka karanta wa matar ƙunshin tuhumar da ake mata ta amsa nan take, ta kuma shaidawa Alkalin kotun cewar tun farko auren dole akayi mata, kuma shi mai gidan nata duk da yasan cewar bata kaunarsa amma kullum sai ya ɓata mata rai.

Mai Shari’a Mansur Yola ya ayyana cewar za a yi hukunci ranar 11/6/2024 dan gudun nama ya dawo romo ɗanye, tunda dai ance Abubakar din yana kwance a asibiti yana ci gaba da samun kulawar likitoci.

Kotun ta kuma umarci a ajiye matar a gidan gyaran hali zuwa waccan ranar da aka sanye domin yanke hukuncin.

Wakilunmu Yusuf Nadabo Ismail ya so zantawa da matar da ake zargi da yankewa mijin nata maƙarfafa, sai dai dogarawan gidan gyaran hali sun shiga tsakani, hakan ya sa lamarin ya gagara.

Manta Sabo

Kotu ta ɗaure wani Matashi kan ji wa mahaifiyar sa rauni da Wuƙa a Kano

Published

on

Wata kotun Majistret mai lamba 44 a Kano, ƙarƙashin jagorancin mai Shari’a Muhammad Alhaji Isah, ta hori wani matashi da ɗaurin shekara ɗaya ba tare da zaɓin tara ba.

Tunda fari dai matashin mai suna Muhammad Inuwa ɗan unguwa uku, Ƴan Sanda ne suka gurfanar da shi bisa zargin sa da ji wa mahaifiyarsa rauni da Wuka, wanda ya amsa laifinsa nan take.

Yayin zaman kotun ta tambaye shi ko yana da wani hanzari kafin hukunci, inda ya bayyana wa kotun cewar sharrin shaiɗan ne, kuma yana ta’ammali da miyagun Ƙwayoyi.

Kotun ta ayyana ɗaurin watanni 12 babu zaɓin tara a kan matashin, an kuma umarce shi da ya zama mutumin kirki, kamar yadda wakilin gidan rediyon Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Ismail ya ruwaito labarin.

Ko a yan kwanakin nan ma dai sai da hukumar hana sha da fataucin miyagun Ƙwayoyi NDLEA, suka bayyana cewar ta’ammali da miyagun Ƙwayoyi kan jawo wa mutum dana sani.

Continue Reading

Manta Sabo

Zargin ɓata suna: Kotu ta bada Belin Ƴar TikTok Alpha Chales Borno

Published

on

Kotun Majistret mai lamba 17 karkashin jagoranci mai Shari’a Huda Haruna Abdu, ta bayar da belin matashiyar yar Tiktok din nan Alpha Charles, wadda Ƴan Sanda suka gurfanar a gaban bisa zargin ta da laifin ɓata suna.

Ƙunshin zargin ya bayyana cewar Alpha Charles, ta ɓata sunan Sadiya Haruna ta dandalin sada zumunta.

Yayin da aka karanta mata tuhumar ta musanta, kuma lauyoyin da suke kare ta sun roki beli, Inda kotun ta sanya ta a hannun beli a bisa sharadin mutum biyu da za su tsaya mata,

Kazalika, sharuɗan Belin sun bayyana cewa, dole ne masu tsayawar na ɗaya ya zama ɗan uwanta na jini, ɗayan kuma ma’aikacin gwamnati mai mataki na 16, idan ta tsere masu karbar belin zasu ajiyewa kotun Naira dubu ɗari biyar.

Sai dai lauyan Alpha ya bayyana wa kotun cewar, Sadiya Haruna ta ɗauki hoto da bidoyon Alpha a harabar kotun ta kuma yaɗa a dandalin Facebook, tare da wasu maganganu da suke zargi na batanci ne.

A don haka kotun ta nemi mai ƙara Sadiya Haruna, sai dai an neme ta sama ko ƙasa ba a ganta ba, an kuma umarci lauyanta da ya gabatar da ita.

Wakilin Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, kotun ta sanya ranar 28 ga wannan watan Afrilun da ake ciki na shekarar 2025, don ci gaba da sauraron shari’ar.

Continue Reading

Baba Suda

Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.

 

Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.

 

Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Continue Reading

Trending