Connect with us

Manta Sabo

Kotun ta umarci jami’an tsaro da su ƙauracewa zaben ƙananan hukumomin da za’a gudanar a Kano

Published

on

Babbar kotun tarayya mai zamanta a Kano karkashin jagorancin mai Shari’a Simon Amobeda, ta rushe shugabancin hukumar zabe ta jahar Kano Kanseic.

Kotun dai ta ɗauki wannan mataki ne bisa dogaro da hujjojin da áká gabatar mata na rashin cancantarsu, kasancewarsu ƴan Siyasa kuma suna ɗauke da katin Jam’iyyar NNPP.

Cikin wata kara wadda Aminu Aliyu Tiga da Jam’iyyar APC suka shigar suna rokon kotun da ta rushe su.

Kotun ta kuma umarci jami’án tsaro da su ƙauracewa zaben ƙananan hukumomin da za’a gudanar tare da umartar hukumar zabe ta kasa INEC, da kada ta bayar da kayan zaben.

A ranar Asabar ne dai 26 ga watan Oktoban 2024, za’a gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi 44 da ke faɗin jihar Kano.

Manta Sabo

Zargin Kisa: Kotu ta aike da Matashi gidan Yari a Kano

Published

on

Kotun Majistret mai lamba 16 ƙarƙashin jagorancin mai Shari’a Alkasim Nasib Ɗan Fillo, ta aike da wani matashi gidan gyaran hali bisa zargin sa da laifin kisan kai.

Tunda fari, Ƴan Sanda ne suka gurfanar da matashin suna zargin sa da laifin haɗa baki da fashi da makami, da kuma laifin kisan kai.

Ƙunshin zargin ya bayyana cewar, a ranar 5 ga wannan watan na Mayun 2025, ne matashin mai suna Aliyu Umar, suka haɗa baki da wasu matasa waɗanda a yanzu sun tsere, inda suka shiga gidan wani mutum mai suna Muhammad Shehu.

An yi zargin cewa bayan sun shiga gidan mutumin sun yi amfani da muggan makamai suka yi masa fashin wayar Salula, daga ƙarshe an zargi cewa sun soka masa Wuƙa a Maƙogoro har rai ya yi halinsa.

Yayin da aka karanta wa matashin ƙunshin zargin ya bayyana cewar ya fahimta, daga nan ne kotun ta bayyana cewar bata da hurumin yin shari’ar kisan kai, a don haka za ta jira shawarar lauyoyin gwamnati.

Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewar, an sanya ranar 26 ga watan gobe don a kara gabatar da matashin a gaban kotu.

Continue Reading

Manta Sabo

Kotu ta tura Amarya da Angon ta gidan Yari a Kano

Published

on

Babbar kotun shari’ar Musulunci da ke zamanta a Post Office, a Kano, ƙarƙashin jagorancin mai Shari’a Munzali Tanko Soron Ɗinki, ta aike wata mata da wani mutum gidan gyaran hali zuwa Mako ɗaya, bisa zargin su da Aure akan Aure.

 

Tunda fari wani magidanci ne ya maka matarsa da wani mutum da ya same shi a ɗakinsa a gaban kotu, ko da dai matar ta ce wai wanda mijin nata ya gani shima mijinta ne.

Lamarin dai ya faru ne a unguwar Tudun Murtala, inda mai ƙarar ya zo gidan matarsa kasancewar yanada wasu matan, sai ya sami wani mutum a kwance akan gadan matar, inda nan take ya tambaye shi waye shi? sai matar ta ce ɗan uwanta ne, hakan ya sa ya gayyato Maƙota su ka zo domin su shaida faruwar lamarin.

Daga bisani ne kuma ya garzaya babbar kotun shari’ar Musulunci da ke Post Office a jihar Kano, ƙarƙashin mai shari’a Munzali Tanko Soron Ɗinki, inda ya yi ƙarar sabon mijin da matar.

Mutumin ya faɗawa kotun cewar shekararsu shida ke nan da Aure a tsakanin su, amma kwatsam sai ya sami wani a ɗakinta, kuma ya ce kwana biyu tsakani ya yi mu’amular Aure da ita.

Sai dai sabon mijin ya ce matar ta faɗa masa bata da Aure, hakan ya sa ya tura wakilansa aka biya dubu ɗari a matsayin sadaki har aka ɗaura musu auren.

 

Ko da Kotu ta wai-wayi matar ta ce ai babu aurensa a kanta bayan samun magana mai karo da juna, a nan ne mai Shari’a ya tambayi asalin waliyinta, inda shi kuma ya ce bai san ta yi wani auren ba.

Hakan yasa kotu ta bukaci ta rantse akan ya saketa sai dai ta ce Eh, aka tambayeta ko za ta rantse ta ce A’a, akace shi tsohon mijin zai rantse ya ce zai rantse, nan take ta ce ba za ta bari ya rantse ba.

Daga bisani kotun ta buƙaci a turasu wajan yan sanda sannan matar ta ce za ta faɗi gaskiya.

 

Matar ta faɗawa kotun cewar tabbas ta yi aure akan Aure, a don haka take neman afuwa, a nan ne mai Shari’a ya aike da matar da sabon mijin gidan gyaran hali har zuwa sati daya domin yi mata hukunci, kamar yadda wakilinmu Aminu Abdu Baka Noma ya ruwaito.

Continue Reading

Manta Sabo

Kotu ta yi umarnin a kamo wani Dagaci a Kano

Published

on

Babbar kotun Shari’ar Muslunci da ke zaman ta a Rijiyar Lemo a nan Kano, ta yi umarnin yansanda su kamo mata dagacin garin Iya malam Lawan Ibrahim.

Tun da farko wani mutum ne mai suna Nura Musa Inuwa mazaunin Katsinawa, ya shigar da ƙara yana da’awar cewa ya sayi gona a hannun dagacin amma daga baya ya samu cewar dagacin ya sayar wa da wani mutum daban gonar.

A zaman dai, kotun ta yi umarnin a kamo mata dagacin a karkashin Shari’a mai lamba Cv/373/2024.

 

Wakilin Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Ismail, ya tuntuɓi dagacin ta wayar Salula, amma bai samu damar ɗagawa ba, ya kuma aike masa gajeren saƙo amma har zuwa lọkacin hada wannan labarin ba mu ji daga gare shi ba.

Continue Reading

Trending