Connect with us

Labarai

Maganin cutar Lassa da abun da yake kawo ta

Published

on

Shugaban Kungiyar jami’an lafiya a jihar Kano, Salman Adamu, ya shawarci al’umma da su kara kulawa da muhallisu domin kaucewa kamuwa da cutar Lassa.

Sulaiman Adamu, ya bayyana hakan ne jim kadan bayan kammala shirin Wannan Rayuwa na Gidan Rediyon Dala a ranar Alhamis, yayin tattaunawa a kan cutar ta Lassa wanda a cikin makon nan a ka samu rahoton bullarta a asibitin koyarwa na Mallam Aminu Kano (AKTH).

Ya na mai cewa “Kulawa da muhallin na mu ya kan taimaka musamman wajen kaucewa kamuwa da cutar ta Lassa da a ke fama da ita a wannan lokaci. A kan kamu da cutar Lassa ne ta hanyar yawun Beraye da kuma karancin tsaftar muhalli da a kan samu wasu mutanen na yi”. Inji Sulaiman Adamu.

Ko a cikin makonnan sai da gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da bular cutar zazzabin Lassa a jihar Kano, amma ta ce ta na kokarin dakile cutar tare da hana ganin ta yadu a fadin jihar baki daya.

Kwamishinan lafiya na jihar, Dr Aminu Ibrahim Tsanyawa ne ya tabbatar da hakan a yayin ganawa da manema labarai.

Ya ce” Mun tabbatar da bullar cutar ta Lassa a Kano, kuma wannan cuta an fara samun bullar ta ne a shekarar 1969 a wani kauyen Lassa dake jihar Borno harma ta yi sanadiyar mutuwar jami’an lafiya na asibiti, kuma daga nan ne ma cutar ake kiran ta da suna Lassa. Cutar mai dauke da kwayar cuta ta mai zafin zazzabi mai tsananin gaske wanda ake kira a turance ‘Viral Hemorrhagic Fever’ wato (VHF) a takaice”.

“Kuma cutar an samu bullar ta a wasu sassan jihohin kasar nan guda (8) wadanda suka hadar da Bauchi,Ondo,Edo,Ebonyi,Taraba,Ogun,Pilateau da kuma jihar Kano a yanzu wadanda kaso 20 kawai aka samu a Kano sauran kuma kaso 60. Kuma ina fada mu ku cewa cutar an samu barkewar ta a ranar 20 ga watannan da muke ciki, kuma ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta tura jami’an ta da suke kula da cututtuka na karamar hukumar Tarauni, an kuma tabbatar cewa wasu likitoci 2 da jami’ar kula da lafiya sun kamu da cutar kuma wanda aka gwada kwayar cutar a dakin gwaji na Gaduwa dake Abuja kuma an tabbatar da bullar cutar ta Lassa”.

“A don haka gwamnatin jihar Kano, ta ware cibiyar kula da cutar ta Yar Gaya wanda yanzu haka a bude take, da sauran dukannin wuraren kiwon lafiya domin ganin an kare yaduwar cutar, sannan kuma nan gaba kadan zamu fara wayar da al’umma yadda zasu kare kansu ta hanyar kafafan gidajen rediyo tare da masu rike da masarautun gargajiya da limamai yadda zasu fadakar da al’umma kan cutar, sannan ga kuma lambobin da za a kirawo kai tsaye dazarar an ji wani alamu na zazzafan zazzabi, 08039704476, 08034988560, 08050595019, 08176673447”. Inji Kwamishinan lafiya na jihar Kano, Dr Aminu Ibrahim Tsanyawa

Yanzu haka dai mutane kusan 292 su ke a killace sakamon wadanda sune suka yi mu’amala da masu cutar ta Lassa.

 

 

 

Labarai

Kisan gillar Edo: A gaggauta nemawa mutanen da aka kashe haƙƙin su, ko mu ɗauki Mataki bisa doka – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Rights Network, ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta Kano da kuma ta jihar Edo, da gaggauta neman haƙƙin Mafarautan nan ƴan asalin jihar Kano waɗanda aka yi wa kisan gilla a garin Uromi na jihar Edo.

Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Gambo Madaki shi ne ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a ranar Litinin, lokacin da yake tsokaci kan kisan sama da Mafarauta 16 a jihar Edo, waɗanda suka taho daga jihar Ribas za su dawo gida Kano.

Ya ce baya ga ɗaukar matakin lalubo waɗanda suka aikata rashin imanin, akwai buƙatar a ɗauki mummunan mataki akan su don daƙile afkuwar irin hakan a gaba.

Rahotanni sun bayyana cewa wasu ɓatabgari ne su ka damke wadanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu a ranar Alhamis.

Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da dama ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.

A cewar Gambo Madaki, baya ga batun kafa kwamiti da gwamnatin Kano ta yi akan wannan batun, ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara bibiyar lamarin da kan sa, don ganin an ɗauki matakin da ya dace akan kisan gillar ko kuma su ɗauki mataki bisa doka.

Continue Reading

Labarai

Mun baza jami’an mu lungu da saƙo don samar da tsaro yayin bikin Sallah a Kano – Anty Snaching Phone

Published

on

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye, ta Anty Snaching Phone, ta ce ta baza jami’an ta kusan dubu ɗaya da za su shiga lungu da saƙo na jihar nan, domin samar da tsaro a yayin bukukuwan ƙaramar Sallah.

Kwamandan rundunar a nan Kano Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da Freedom Radio, ya kuma ce jami’an su za su yi duk mai yiyuwa wajen daƙile ayyukan ɓata garin da ke shirin tayar da hankalin al’umma yayin bikin sallar.

“Daga cikin jami’an mu da za su samar da tsaron akwai na cikin kayan mu da kuma na farin kaya, kuma sun fara bazama guraren da mu ka tura su tun cikin kin daren Asabar ɗin nan kuma za su yi aiki cikin ƙwarewa kamar yadda suka samu horo, “in ji Inuwa”.

Sharaɗa, ya kuma ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa kulawar shugaban kwamitin karta-kwana da ke yaƙi da miyagun ɗabi’u da gwamnan ya kafa ƙarkashin Dakta Yusuf Ƙofar Mata.

Wannan dai na zuwa ne yayin da za’a gudanar da sallar Idi, ta ƙaramar Sallah a ranar Lahadin nan a Najeriya, da Jamhuriyyar Nijar da ƙasar Saudiyya, da ma wasu ƙasashen Duniya.

Continue Reading

Labarai

Za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 – Masani

Published

on

Wani masanin ilmin Taurari da ke jihar Kano a arewacin Najeriya, Mallam Nasir Falaki Al-Kanawi, ya ce za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 saboda watan Shawwal ba zai ganu ba a ranar Asabar, don da ƙarfe 11:58 na safe za a haifi jinjirin watan kuma zai faɗi 06:48 na Yamma.

Mallam Nasiru Alfaki Al-Kanawi ya bayyana hakan ne a wani taƙaitaccen jawabi da ya yi wa gidan rediyon Dala FM Kano a ranar Juma’a 28 ga watan Maris ɗin shekarar 2025.

Alfalaki ya kuma ce watan zai faɗi ne da ƙarfe 6:48 na yamma mintuna kasa da 10 kenan bayan faduwar Rana, kasancewar ranar ƙarfe 6:37 na yamma za ta fadi.

Ya ci gaba da cewa to wannan dalilin ne zai sa watan ba zai ganu ba, ko da kuwa da Na’ura ne kasancewar bai samu wadataccen hasken da zai ɗosana daga ranar ba, wanda aƙalla yana buƙatar awanni 13 zuwa 16 daga haifeshi kafin ace an iya ganinsa, Allah shi ne mafi sani Mai iko akan komai.

Continue Reading

Trending