Labarai
Maganin cutar Lassa da abun da yake kawo ta
Shugaban Kungiyar jami’an lafiya a jihar Kano, Salman Adamu, ya shawarci al’umma da su kara kulawa da muhallisu domin kaucewa kamuwa da cutar Lassa.
Sulaiman Adamu, ya bayyana hakan ne jim kadan bayan kammala shirin Wannan Rayuwa na Gidan Rediyon Dala a ranar Alhamis, yayin tattaunawa a kan cutar ta Lassa wanda a cikin makon nan a ka samu rahoton bullarta a asibitin koyarwa na Mallam Aminu Kano (AKTH).
Ya na mai cewa “Kulawa da muhallin na mu ya kan taimaka musamman wajen kaucewa kamuwa da cutar ta Lassa da a ke fama da ita a wannan lokaci. A kan kamu da cutar Lassa ne ta hanyar yawun Beraye da kuma karancin tsaftar muhalli da a kan samu wasu mutanen na yi”. Inji Sulaiman Adamu.
Ko a cikin makonnan sai da gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da bular cutar zazzabin Lassa a jihar Kano, amma ta ce ta na kokarin dakile cutar tare da hana ganin ta yadu a fadin jihar baki daya.
Kwamishinan lafiya na jihar, Dr Aminu Ibrahim Tsanyawa ne ya tabbatar da hakan a yayin ganawa da manema labarai.
Ya ce” Mun tabbatar da bullar cutar ta Lassa a Kano, kuma wannan cuta an fara samun bullar ta ne a shekarar 1969 a wani kauyen Lassa dake jihar Borno harma ta yi sanadiyar mutuwar jami’an lafiya na asibiti, kuma daga nan ne ma cutar ake kiran ta da suna Lassa. Cutar mai dauke da kwayar cuta ta mai zafin zazzabi mai tsananin gaske wanda ake kira a turance ‘Viral Hemorrhagic Fever’ wato (VHF) a takaice”.
“Kuma cutar an samu bullar ta a wasu sassan jihohin kasar nan guda (8) wadanda suka hadar da Bauchi,Ondo,Edo,Ebonyi,Taraba,Ogun,Pilateau da kuma jihar Kano a yanzu wadanda kaso 20 kawai aka samu a Kano sauran kuma kaso 60. Kuma ina fada mu ku cewa cutar an samu barkewar ta a ranar 20 ga watannan da muke ciki, kuma ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta tura jami’an ta da suke kula da cututtuka na karamar hukumar Tarauni, an kuma tabbatar cewa wasu likitoci 2 da jami’ar kula da lafiya sun kamu da cutar kuma wanda aka gwada kwayar cutar a dakin gwaji na Gaduwa dake Abuja kuma an tabbatar da bullar cutar ta Lassa”.
“A don haka gwamnatin jihar Kano, ta ware cibiyar kula da cutar ta Yar Gaya wanda yanzu haka a bude take, da sauran dukannin wuraren kiwon lafiya domin ganin an kare yaduwar cutar, sannan kuma nan gaba kadan zamu fara wayar da al’umma yadda zasu kare kansu ta hanyar kafafan gidajen rediyo tare da masu rike da masarautun gargajiya da limamai yadda zasu fadakar da al’umma kan cutar, sannan ga kuma lambobin da za a kirawo kai tsaye dazarar an ji wani alamu na zazzafan zazzabi, 08039704476, 08034988560, 08050595019, 08176673447”. Inji Kwamishinan lafiya na jihar Kano, Dr Aminu Ibrahim Tsanyawa
Yanzu haka dai mutane kusan 292 su ke a killace sakamon wadanda sune suka yi mu’amala da masu cutar ta Lassa.
Labarai
Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa
An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.
Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.
Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.
Hangen Dala
Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano
A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.
Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.
Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.
Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.
Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.
Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito
Labarai
Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure
Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.
Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.
Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.
Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.
-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi4 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su