Labarai
Maganin cutar Lassa da abun da yake kawo ta

Shugaban Kungiyar jami’an lafiya a jihar Kano, Salman Adamu, ya shawarci al’umma da su kara kulawa da muhallisu domin kaucewa kamuwa da cutar Lassa.
Sulaiman Adamu, ya bayyana hakan ne jim kadan bayan kammala shirin Wannan Rayuwa na Gidan Rediyon Dala a ranar Alhamis, yayin tattaunawa a kan cutar ta Lassa wanda a cikin makon nan a ka samu rahoton bullarta a asibitin koyarwa na Mallam Aminu Kano (AKTH).
Ya na mai cewa “Kulawa da muhallin na mu ya kan taimaka musamman wajen kaucewa kamuwa da cutar ta Lassa da a ke fama da ita a wannan lokaci. A kan kamu da cutar Lassa ne ta hanyar yawun Beraye da kuma karancin tsaftar muhalli da a kan samu wasu mutanen na yi”. Inji Sulaiman Adamu.
Ko a cikin makonnan sai da gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da bular cutar zazzabin Lassa a jihar Kano, amma ta ce ta na kokarin dakile cutar tare da hana ganin ta yadu a fadin jihar baki daya.
Kwamishinan lafiya na jihar, Dr Aminu Ibrahim Tsanyawa ne ya tabbatar da hakan a yayin ganawa da manema labarai.
Ya ce” Mun tabbatar da bullar cutar ta Lassa a Kano, kuma wannan cuta an fara samun bullar ta ne a shekarar 1969 a wani kauyen Lassa dake jihar Borno harma ta yi sanadiyar mutuwar jami’an lafiya na asibiti, kuma daga nan ne ma cutar ake kiran ta da suna Lassa. Cutar mai dauke da kwayar cuta ta mai zafin zazzabi mai tsananin gaske wanda ake kira a turance ‘Viral Hemorrhagic Fever’ wato (VHF) a takaice”.
“Kuma cutar an samu bullar ta a wasu sassan jihohin kasar nan guda (8) wadanda suka hadar da Bauchi,Ondo,Edo,Ebonyi,Taraba,Ogun,Pilateau da kuma jihar Kano a yanzu wadanda kaso 20 kawai aka samu a Kano sauran kuma kaso 60. Kuma ina fada mu ku cewa cutar an samu barkewar ta a ranar 20 ga watannan da muke ciki, kuma ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta tura jami’an ta da suke kula da cututtuka na karamar hukumar Tarauni, an kuma tabbatar cewa wasu likitoci 2 da jami’ar kula da lafiya sun kamu da cutar kuma wanda aka gwada kwayar cutar a dakin gwaji na Gaduwa dake Abuja kuma an tabbatar da bullar cutar ta Lassa”.
“A don haka gwamnatin jihar Kano, ta ware cibiyar kula da cutar ta Yar Gaya wanda yanzu haka a bude take, da sauran dukannin wuraren kiwon lafiya domin ganin an kare yaduwar cutar, sannan kuma nan gaba kadan zamu fara wayar da al’umma yadda zasu kare kansu ta hanyar kafafan gidajen rediyo tare da masu rike da masarautun gargajiya da limamai yadda zasu fadakar da al’umma kan cutar, sannan ga kuma lambobin da za a kirawo kai tsaye dazarar an ji wani alamu na zazzafan zazzabi, 08039704476, 08034988560, 08050595019, 08176673447”. Inji Kwamishinan lafiya na jihar Kano, Dr Aminu Ibrahim Tsanyawa
Yanzu haka dai mutane kusan 292 su ke a killace sakamon wadanda sune suka yi mu’amala da masu cutar ta Lassa.
Labarai
Rahoto: Mu nisanci abinda Allah Ya hana domin samun saukin rayuwa – Limamin Tukuntawa

Limamin masallacin juma’a na Masjidul Kuba da ke unguwar Tukuntawa a jihar Kano, Malam Ahmad Ali, ya ce, al’umma su duba tsakanin su da Allah tare da nisantar abinda ya hana, domin saukin tsadar rayuwa.
Malam Ahmad Ali, ya bayyana hakan ne, yayin da yake yiwa wakilin mu na ‘yan Zazu, Ibrahim Abdullahi Soron Dinki, Karin bayani dangane da abinda hudubar da ya gabatar ta kunsa.
Akwai cikakken bayanin hudubar a muryar da ke kasa.
Labarai
Rahoto: Rubutu na da muhimmanci a mu’amalar bashi – Limamin Bompai

Limamin masallacin juma’a na Shelkwatar rundunar ‘yan sandan jihar Kano da ke unguwar Bompai, SP Abdulkadir Haruna, ya ce, akwai bukatar mu rinka gudanar da mu’amalar bashi yadda addinin musulunci.
SP Abdulkadir Haruna, yana bayyana hakan, a zantawarsa da wakilin mu na ‘yan Zazu, Abba Isah Muhammad, bayar idar da Sallar Juma’a.
Domin jin cikakken rahoton saurari wannan.
Labarai
Rahoto: Matashi ya yi yunkurin cinye tabar Wiwin da aka kama shi da ita a hanyar kotu

Ana zargin wani matashi ya yi yunkurin hadiye tabar Wiwi da miyagun kwayoyi da aka kama shi da ita a hanyar kotu.
Tunda fari jami’an tsaron, sun kama matasahin da zargin samun sa da kayan maye, inda yake boye da wasu basu sani ba, kafin kuma a kai shi kotu, ya ciro su yana yunkurin hadiye wa.
Wakilin mu na ‘yan Zazu, Ibrahim Abdullahi Soron Dinki yana da cikakken rahoton.
-
Nishadi3 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai3 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai2 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Nishadi3 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai2 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Lafiya2 months ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi3 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai3 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano