Connect with us

Labarai

An yi garkuwa da wani babur a Kano kuma an bukaci kudin fansa

Published

on

Wanda ake zargin ya dai dauki babur din ne roba-roba kirar Lifan ya kuma ga takardun makarantar mai baburdin a cikin akwatun ajiye kaya wato (booth) harda lambar waya a cikin babur din nan ta key a kuma dauki lambar ya buga ya kirawo mai babur din inda ya nemi a bashi kudin fansa Naira dubu goma sha biyar (15,000) kafin ya bada babur din.

Lamarin da ya sanya nan ta ke mai babur din mai suna Ibrahim ya nemi mai garkuwa da babur din ya bashi lambar asusun san a banki, bayan ya tura kudin a ka sanar da jami’an tsaro suka bibiye shi wato (tracking) din asusun bankin a ka kuma sami nasarar kama shi a Sabon Gari Bata a jihar Kano.

wata abokiyar aikin Ibrahim wacce suka yi waya da wannan matashin da ake zargi da garkuwa da babur din ta ce” A matsayin mahaifiyar Ibrahim na je wa mai garkuwa da babur din amma ya ce shifa balaifin sa bane”.

Sai dais hi mamallakin babur din Ibrahim ya ce “To da ya ke hausawa na cewa rana dubu ta barawo rana daya tak tamai kaya, kuma idan daraban shan duka bari bata magani, ashe asusun bankin wani mai sana’ar bada kudi na turawa wato (POS) na karbo wanda kuma ba mu da alaka ta sanaiya da shi”. Inji Ibarhim.

Bincike dai ya tabbatar da cewa wannan matashin mai garkuwa da babur ya siyar da babur din a kan kudi Naira dubu goma shabiyar, duk da dai kokarin da mukayi na zantawa da wannan matashi al’amari ya faskara, dafatan Allah ya tsari gatari da sarar shuka.

Wakilimmu Mu’azu Musa Ibrahim yarawaito cewa, babur din an siyar da shi ne a kasuwar farm center dake Kano, bayan tarkon da aka danawa matashin na farko a ka kuma kara kama wani matashin wanda shi ma ya siyar da babur din, tahanyar.

Dubun dayan matashin ya cika ne bayan wanda ake zargin na farko ya buga masa waya ya sanar da shi cewa an samu wanda zai kara siyan baburin a kan kudi naira dubu arba’in (40000) duk da sun siyar da babur din suka sake zuwa da niyar karbar wannan kudi naira (40000) domin karawa a kan wancan dubu (15000) baya ga dubu (15000) din da suka nemi kudin fansa tun da farko.

Labarai

Zamu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ƴan Jarida – Hukumar Zaɓe ta Kano

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSEC, ta sha alwashin aiki kafaɗa-kafaɗa da ma’aikatan Jarida, musamman ma da zaɓen ƙananan hukumomin jihar nan 44 da ke tafe.

Sabon shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Manumfashi, ne ya bayyana hakan, yayin ziyarar da tawagar ƙuniyar matasan ƴan Jarida, ta Kano Youth Journalist Forum, suka kai masa a ofishin sa yau Alhamis, yayin da ya shafe kwanaki huɗu da kama aiki.

Ya kuma ce, za su yi aiki da ma’aikatan Jarida musamman ma yayin gudanar da ayyukan zaɓen ƙananan hukumomin Kano 44, da ke tafe, domin wayar da kan al’umma da ma samun nasara yayin zaɓen da ma bayan sa.

Farfesa Manumfashi, ya kuma ƙar da cewa, akwai buƙatar kowa ya bayar da tasa gudummawar a harkar zaɓe, domin kuwa yanzu haka suna ci gaba da aiki wajen shirya zaɓen ƙananan hukumomin.

Da yake nasa jawabin shugaban ƙungiyar matasa ƴan Jaridar ta jihar Kano Musa Zangina Adam, ya ce sun kai ziyarar ne, domin su ƙulla alaƙar aiki a tsakanin su da hukumar, bisa yadda kowanne ɓangare yake buƙatar juna, tare kuma da bayar da gudunmawar da ya kamata.

Zangina, ya kuma ce a shirye ƙungiyar su take wajen ci gaba da bibiyar al’amuran da suka shafi al’umma, tare da nusar da mahukunta dan ganin an wadata su da kayayyakin more rayuwa.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Trending