Connect with us

Labarai

An yi garkuwa da wani babur a Kano kuma an bukaci kudin fansa

Published

on

Wanda ake zargin ya dai dauki babur din ne roba-roba kirar Lifan ya kuma ga takardun makarantar mai baburdin a cikin akwatun ajiye kaya wato (booth) harda lambar waya a cikin babur din nan ta key a kuma dauki lambar ya buga ya kirawo mai babur din inda ya nemi a bashi kudin fansa Naira dubu goma sha biyar (15,000) kafin ya bada babur din.

Lamarin da ya sanya nan ta ke mai babur din mai suna Ibrahim ya nemi mai garkuwa da babur din ya bashi lambar asusun san a banki, bayan ya tura kudin a ka sanar da jami’an tsaro suka bibiye shi wato (tracking) din asusun bankin a ka kuma sami nasarar kama shi a Sabon Gari Bata a jihar Kano.

wata abokiyar aikin Ibrahim wacce suka yi waya da wannan matashin da ake zargi da garkuwa da babur din ta ce” A matsayin mahaifiyar Ibrahim na je wa mai garkuwa da babur din amma ya ce shifa balaifin sa bane”.

Sai dais hi mamallakin babur din Ibrahim ya ce “To da ya ke hausawa na cewa rana dubu ta barawo rana daya tak tamai kaya, kuma idan daraban shan duka bari bata magani, ashe asusun bankin wani mai sana’ar bada kudi na turawa wato (POS) na karbo wanda kuma ba mu da alaka ta sanaiya da shi”. Inji Ibarhim.

Bincike dai ya tabbatar da cewa wannan matashin mai garkuwa da babur ya siyar da babur din a kan kudi Naira dubu goma shabiyar, duk da dai kokarin da mukayi na zantawa da wannan matashi al’amari ya faskara, dafatan Allah ya tsari gatari da sarar shuka.

Wakilimmu Mu’azu Musa Ibrahim yarawaito cewa, babur din an siyar da shi ne a kasuwar farm center dake Kano, bayan tarkon da aka danawa matashin na farko a ka kuma kara kama wani matashin wanda shi ma ya siyar da babur din, tahanyar.

Dubun dayan matashin ya cika ne bayan wanda ake zargin na farko ya buga masa waya ya sanar da shi cewa an samu wanda zai kara siyan baburin a kan kudi naira dubu arba’in (40000) duk da sun siyar da babur din suka sake zuwa da niyar karbar wannan kudi naira (40000) domin karawa a kan wancan dubu (15000) baya ga dubu (15000) din da suka nemi kudin fansa tun da farko.

Hangen Dala

Rashin wuta: Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Published

on

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.

Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.

Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.

Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.

Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.

Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.

Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.

Continue Reading

Hangen Dala

Rashin wuta:- Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Published

on

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.

 

Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.

 

Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.

 

Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.

 

Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.

 

Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.

 

Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.

Continue Reading

Labarai

Ci gaba ba ya zuwa sai an samu haɗin kan al’umma – Dagacin Ja’en

Published

on

Dagacin garin Ja’en da ke ƙaramar hukumar Gwale a jihar Kano, Alhaji Isma’il Sa’ad Usman, ya ce hadin kai ne kaɗai zai kawo ci gaba ga kowa ce irin al’umma.

Dagacin ya bayyana hakan ne Jim kaɗan bayan wani taron masu Ruwa da tsaki na Garin Ja’en, wanda Hakimin Gundumar Ɗorayi Barde Kerarriya Alhaji Shehu Kabir Bayero ya shirya, aka gudanar a yankin Ja’en a ƙarshen makon da ya gabata.

“Dukkanin wani ci gaba ba ya zuwa har sai an samu haɗin kan kowa ne bangare na al’umma, “in ji Dagacin”.

Wakilin Dala FM Kano, Ahmad Rabi’u Ja’en ya ruwaito cewa, taron ya samu halartar dukkanin bangarori, na unguwannin Ja’en, da suka haɗar da kungiyar mafarauta da maharba dabma kungiyar malaman makaranta.

Continue Reading

Trending