Connect with us

Labarai

An yi wa matasa fintinkau a karatun Kur’ani –Mallam Ahmad Rufa’i

Published

on

Malamin addinin musulunci a jihar Kano, Mallam Ahmad Rufa’i Mai Kasida, ya ce dole ne al’ummar musulmai musamman ma matasa maza sai sun kara bada himma a wajen neman ilimi, domin rayuwar su ta zama abar koyi a nan duniya dama gobe kiyama.

Mallam Ahmad Rufa’i, ya yi kiran ne a yayin saukar karatun Al’kur’ani mai girma da makarantar Madarasatul Ta’alimul Qur’an Islamiyya dake unguwar Ja’en a yankin karamar hukumar Gwale ta gudanar da saukar karshen makon da ya gabata.

Ya na mai cewa” Kara bada himma da neman ilmin yakan taimakawa matasan wajen kaucewa fadawar su cikin wani hali, sakamakon dole sai da ilimi rayuwa ke samun ci gaba”. Inji Mallam Ahmad.

Da yake nasa jawabin shugaban makarantar, Mallam Aliyu Hamza Hassan, cewa ya yi” Makarantar a mafi yawan lokuta takan fuskanci kalubale daga bangaren iyaye, musamman wajen nuna halin ko in kula da iyayen suke nunawa da karatun ya’yansu a makarantar, kuma wajibi iyaye dasu kara bada kulawa da karatun ya’yan nasu ba tare da gajiyawa ba”. Inji Mallam Aliyu.

Suma wasu daga cikin daliban da suka yi saukar karatun Al’kur’anin wanda suka kasance mata goma sha daya namiji daya, sun bayyana farin cikin su dangane da saukar da sukayi, sannan sun ce za su yi amfani da abun da suka samu.

A yayin saukar dai wakilin mu Hassan Mahmuda Ya’u ya rawaito cewa, al’umma da dama ne suka samu damar halarta daga yankin na Ja’en, daga ciki kuwa akwai mai unguwar Ja’en Yamma (A) Mallam Ya’u Musa Wakili.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending