Connect with us

Labarai

Yadda a ke yanka rakumi

Published

on

Jami’in hulda da jama’a na kasuwar sayar da dabbobi da ke Kofar Na’isa, Kwamared Umar Hamisu Kofar Na’isa ya ce, rashin iya sarrafa naman rakumi wajen dafawa kan sanya shi yin tauri.

Kwamared Umar Hamisu Kofar Na’isa ya bayyana hakan ne a zantawar sa da gidan gidan rediyon Dala ranar Talata.

Ya ce, “Mu nan jihar Kano ba mu saba da yanka rakumi a matsayin abun layya ba, za ka ga idan a ka ce, gida za’a yanka rakumi abun ya zama abun kallo, za’a cika yara da manya an zo kallon yanka rakumi, amma lokaci na tafiya, da ya ke an ce zamani canjawa yake, kusan daga shekaru uku zuwa mutane sun fara fahimtar yanka rakumi, kuma mu na nan mu na bincike a kan batun shin tsakanin rakumi da sa wanne yafi nama? Kamar mu yanzu idan kwastoma ya zo mu na wasa kasuwar mu da cewar, rakumin dubu dari da hamsin zai iya baka naman sa na dubu dari da tamanin”.

Kwamared Umar, ya kuma ce, “Rashin fahimta ne, a na yawan cewa naman rakumi yafi tauri, tunda an fi sabawa da yanka sa, ta bangaren sarrafawa ne idan har uwar gida, ko kuma wadanda za su sarrafa naman sun goge da yadda za su iya sarrafa naman rakumi, to ba za ka iya banbance naman rakumi da naman sa ba, domin za ka iya zuwa kasuwa ka sayi naman rakumin ba kasan shi ba ne ba”.

Ya kara da cewa, “Rakumi ba kayar da shi a ke yi kamar sa ba, a kan dan yi masa ‘yan dabaru ya kwanta, idan ma bai kwanta ba za’a sa igiyoyi a kafafunsa guda biyu a ja su, a rike kafafun sa guda biyu na gaba sai a hade su a sa igiya a daure tsakanin gwiwar hannun, sai kafafun ya kwanta, shi ba sai an kwantar da shi ya yi rigingine ba, shi zaman rakumi tankwashe kafa ya ke yi, kafafun da ya tankwashe sai a sa igiya, wannan dogon wuyan na sa sai a jawo igiya kan ya lakwanshe ya hadu da gangar jiki sai a daure kan”.

Kazalika, ya kuma ce, “Yadda ake yanka rakumi ba yadda ake yanka sa ba ne, shi ba tsakiyar wuyan sa a ke yanka wa ba, shi kuma rakumi a na yanka shi ta tsakanin wuyan na sa da gangar jiki, akwai wani rami da ake sa mun wuka mai tsini sai a caka a jata gefe da gefe, daga nan rakumi ya yanku, sai kuma fida, shi kuma rakumi ta baya ake fede shi”. A cewar Kwamared Umar Kofar Na’isa

Wakilin mu Tijjani Adamu ya rawaito cewar, Kwamared Hamisu ya kuma ce, babban rakumi wanda a ka saba da hawan sa, yafi saukin yankawa a kan matashin rakumi wanda yanka shi ya ke bayar da wahala.

 

Labarai

Wahalar Fetur: Fadar shugaban ƙasa kiyi wani abu dan mutane su samu sauƙi – Ƙungiyar Nothern Concern Soliderity

Published

on

Yayin da al’umma ke ci gaba da fuskantar wahalar man fetur a ƙasar nan, ƙungiyar da ta damu da abubuwan da suka shafi arewacin ƙasar nan ta Northern Concern Soliderity, ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi abinda ya dace dan ganin mutane sun samu wani sauƙi.

Babban jami’in gudanarwar ƙungiyar, kuma sakataren riƙo na zauren gamayyar kungiyoyin Arewacin Najeriya, Kwamared Saddat Usman Maiyaƙi, ne ya bayyana hakan a zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, lokacin da yake nuna takaici kan irin wahalar da al’ummar ƙasa suke sha wajen shan man Fetur a gidajen man.

Ya ce duba da halin matsin rayuwar da al’umma suka samu kansu a ciki, akwai buƙatar shugabanni da masu ruwa da tsaki su kawo ƙarshen wahalar man Fetur ɗin da aka fama da ita.

Kwamared Saddat Maiyaƙi, ya kuma haƙurƙurtar da al’ummar ƙasar nan kan halin ƙuncin rayuwar da suka samu kai a ciki, inda ya yi fatan komai ya zo karshe cikin ƙanƙanen lokaci.

Continue Reading

Labarai

Abin takaici ne yadda ake fuskantar ƙarancin ruwan Sha a sassan jahar mu – Gwamnan Kano.

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya nuna rashin jin daɗin sa bisa yadda ake samun ƙarancin Ruwan Sha, a wasu daga cikin sassa jihar Kano.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi ga manema labarai, a lokacin a ya kai ziyarar gani da ido, matatar Ruwa da ke Tamburawa a yammacin yau Juma’a, a ƙokarin sa na na gyara ɓangaren ruwan a cikin garin Kano.

Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kuma sha alwashin tabbatar wa al’umma cewar, gwamnatin sa za ta yi aiki ba dare ba rana domin tabbatar da isasshen ruwan Sha ga al’ummar jihar Kano.

Gwamnan ya ƙara da ce a lokacin da suka zo ba sufi mako biyu ba suka samar da ingantaccen Ruwan sha, wanda ya rinƙa shiga cikin lunguna da Sako na sassan jihar.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar hukumar Tofa ta dakatar da sayar da Burtalai a wasu garuruwan ta

Published

on

Biyo bayan kokawar da wasu Fulani Makiyaya suka yi kan yadda wasu suka gididdiba burtalai yayin da aka siyarwa Manoma, a garuruwan Yanoko da Gajida da kuma Dindere, yanzu haka ƙaramar hukumar Tofa ta dakatar da taɓawa, ko kuma sayar da dukkanin Burtalan kiwon shanun ba tare da ɓata lokaci ba.

Shugaban riƙon ƙaramar hukumar ta Tofa Abubakar Sulaiman Mai Rogo, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da aka aikowa Dala FM Kano, a ranar Alhamis.

Mai Rogo, ya kuma ce ƙaramar hukumar ba ta da hannu a kan taɓa dukkan guraren, a dan haka sun dakatar da dukkanin yunƙurin taɓa Burtalan har sai shugabanni na kwamitin ƙasa sun kammala bincike wanda yanzu haka ake ci gaba da yi.

Da yake nuna jin daɗin sa kan matakin dakatarwar, amadadin Fulanin garuruwan, shugaban ƙingiyar Funali Makiyaya ta Gan Allah, Ahmad Shehu Gajida, yabawa gwamnatin jihar Kano, da kuma ƙaramar hukumar ta Tofa ya yi, bisa karɓar koken su da suka akai.

A baya-bayan nan ne dai a zantawar Dala FM Kano, da wasu Funalani Makiyaya mazauna garuruwan Yanoko da Gajida da kuma Dindere, suka koka kan yadda aka gididdiba burtalan a yankunan nasu aka siyarwa manema, lamarin da suka ce ka iya sawa su rasa guraren da za suyi kiwon shanun su wanda hakan babbar barazana ce a gare su.

Continue Reading

Trending