Connect with us

Labarai

Iyayen yaran nan da aka sace sun zargi gwamnatin Kano da kin daukar mataki

Published

on

Shekara guda kenan, da jami’an ‘yan sanda suka gano matsalar batan yaran da ake fama da su a jihar Kano da ke arewacin Najeriya, inda ake zuwa da su kudancin kasar.

Ana dai zargin cewa yaran da ake sacewa zuwa kudancin kasar, ana sauya musu suna da kuma addini.

Daga lokacin da aka gano batan yaran ne gwamnatin jihar ta kafa wani kwamiti na musamman da zai gudanar da binciken zargin batan yaran.

To sai dai kwatsam, iyayen yaran da aka sace sun bayyana takaicin su kan yadda gwamnati ta nuna halin ko in kula da halin da suke ciki.

Iyayen dai na zargin gwamnatin jihar da rashin daukar matakan da suka dace wajen binciko inda yaransu suke, duk da cewa akwai sama da guda dari da har yanzu ba a san inda suke ba.

“Gaskiya, mun fara yanke kauna da matakan gwamnatin, saboda ‘yayan talakawa ne ya sanya gwamnatin ta yi biris da batun ‘yayanmu.” In ji Zainab Giginyu

Wadannan magidanta da suka yi tattaki mazan su da matan su zuwa Dala FM, sun bayyana cewar akwai sauran yayansu sama da guda dari a yankin kudancin kasar da aka sace, amma da yawan wadanda aka zarga da satar ma an bayar da belisu suna cigaba da rayuwar su cikin farin ciki yayin da wata ma da aka bayar da belin ta ta arce.

“Muna cikin mawuyacin hali, muna rokon gwamnati ta taimaka ta binciko mana yaranmu idan har don mu take aiki, mu ‘yayanmu muke nema ba wani abu muke roko gwamnati ta yi mana ba.” In ji mahaifiyar wata yarinya

A baya dai kungiyar iyayen yaran da suka bata ta ce kwamitin da aka kafa be tuntube su ba, don haka basu da masaniya kan yadda kwamitin yake aikinsa.

Kungiyar ta ce kwamitin bincike da aka kafa tun farko be neme su ba ta yadda za su iya gabatar da bahasin yadda yaransu suka bata.

Malam Salihu Isma’il shine mai magana da yawun iyayen yaran, ya ce suna takaicin yadda gwamnati ta gaza daukar mataki, bayan tsawon shekara guda da batan yaransu.

“Yau tun da aka dawo da yaran nan shekara daya, wasu daga cikin yaran da aka dawo da su, sun ce sun ga ‘yayanmu, wasu ma ajinsu daya. tsawon shekara daya, kwamitin da aka nada har yanzu ko yaro guda daya be dawo mana da shi ba.”

Malam Salihu ya ce wasu daga cikin iyayen yara, yanzu haka suna fama da ciwon mutuwar barin jiki, wasun su kuma sun mutu saboda takaicin batan yaran nasu.

A baya-bayan nan ne kwamitin ya gabatar da rahoton bincikensa, duk da cewa kungiyar iyayen yaran ta ce babu wani tuntuba da suka same daga bangaren gwamnati kan wannan batu.

Labarai

An sanya ranar fara ɗibar Maniyyata aikin Hajjin 2025, daga Kano zuwa ƙasar Saudiyya

Published

on

Yayin da aikin hajjin bana ke ƙara gabatowa a ƙasa mai Tsarki, hukumar jin daɗin Alhazai ta Jihar Kano, ta shayar da ranar 13 ga watan Mayun 2025, a matsayin ranar farko da za’a fara ɗibar Maniyyata aikin hajjin bana, daga jihar Kano zuwa ƙasar Saudiyya.

Cikin sanarwar da jami’in yaɗa labaran shukumar Sulaiman Abdullahi Dederi ya fitar, ta ce Darakta Janar na hukumar Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ne ya bayyana hakan ranar Asabar, a yayin wata ziyara da ya kai cibiyoyin karatun koyon Aikin Hajj na kananan hukumomin Ungogo da Bichi, a wani bangare na shirin Hajjin shekarar 2025.

 

“Bisa ga jadawalin da Hukumar kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta fitar, cewa Jihar Kano za ta fara jigilar maniyyatan mu zuwa Saudiyya, tare da kamfanin jirgin sama na Max Air a ranar 13 ga Mayu, 2025, “in ji Lamin”.

Ɗanbaffa, ya ƙara da cewa Hukumar ta kammala dukkanin shirye-shiryen da suka kamata tun da wuri, domin tabbatar da cewa an gudanar da jigilar maniyyatan cikin nasara da tsari mai kyau.

 

Da yake nasa jawabin, Shugaban Hukumar, Alhaji Yusif Lawan, ya ja hankalin maniyyata masu niyyar tafiya aikin hajjin, da su rika halartar karatun koyon Aikin Hajjin a kai a kai domin amfanin kansu.

 

Haka kuma, ya gargade su da su kiyaye bin dokoki da ka’idojin na hukumomin Najeriya, da kuma waɗanda Saudiyya suka shimfiɗa domin tafiyar da aikin Hajjin na 2025.

Continue Reading

Labarai

Ba mu san Hamisu Breaker ya saki waƙar Amanata ba – Hukumar tace fina-finai

Published

on

Hukumar tace Fina-finai da Ɗab’i ta jihar Kano ta ce yanzu haka tana kan bincike don gano yadda akai mawakin nan Hamisu Breaker, ya saki sabuwar wakarsa mai suna “Amanata” ba tare da an tantance ta ba.

Mai magana da yawun hukumar Abdullahi Sani Sulaiman, shi ne ya bayyana hakan a wani sakon murya da ya aikowa Dala FM Kano, a ranar Alhamis 24 ga watan Afrilun 2025.

Ya kuma ce aikin dakatar da wakar ba na hukumar Hisbah ba ne na hukumar tace fina-finai ne, amma ba laifi ba ne kasancewar duk hukumomi ne na Gwamnati, a don haka idan hukumar ta Hisbah ta magantu akai babu laifi, domin dama suna aiki kafaɗa da kafaɗa.

A game da wakar ta Hamisu Beraker, mai suna “Amanata”, Abdullahi Sani, ya ce su har yanzu ba su san ta ina wakar ta fita ba tare da an tantance ta ba, amma tuni shugaban hukumar Abba Al-mustapha ya bada umarnin gudanar da bincike akan ta.

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ce dai ta hannun mataimakiyar babban kwamandan ta a ɓangaren mata Dakta Khadijah Sagir Sulaiman, ta yi Allah wa-dai da wakar Hausar mai taken “Amana ta” da mawaki Hamisu Breaker ya rera, inda ta shawarci matasa da su guji sauraren wakar, bisa yadda take ɗauke da abubuwan da ke ƙarfafa aikata alfasha, da kuma amfani da kalmomin batsa a cikin bidiyon ta.

Continue Reading

Hangen Dala

Rashin wuta: Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Published

on

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.

Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.

Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.

Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.

Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.

Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.

Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.

Continue Reading

Trending