Connect with us

Ilimi

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta ƙara wa’adin yajin aiki da ta ke yi

Published

on

Kungiyar Malaman Jami’o’i a ta ƙasa ASUU, ta bayyana matakin tsawaita yajin aikin da take yi har zuwa mako huɗu a nan gaba.

ASUU ta shafe sama da watanni biyar ta na yajin aikin bayan gaza cimma matsaya da gwamnatin tarayya, yanzu kuma gashi ta kara wata daya.

Idan har aka shafe wasu makonni hudu ba a sasanta tsakanin gwamnati da ASUU ba, hakan na nufin ɗaliban jami’o’in sun shafe rabin shekara suna zaman jiran tsammani a gida.

Sanarwar da ASUU ta fitar na dauke da sa hannun Shugaban kungiyar Emmanuel Osodeke, an kuma fitar da ita ne bayan kammala wani zaman gaggaawa na jiga-jigan kungiyar ranar Lahadi a Abuja.

Hakama ASUU ta gode wa ƙungiyar Kwadago ta NLC, da sauran kungiyoyin da suka mara mata baya wurin yin zanga-zangar nuna goyon baya da nufin kawo karshen yajin aikin.

Kungiyar Malaman Jami’ar ta kara da cewa, ta tsawaita yajin aikin ne da mako hudu, lura da cewa, har yanzu gwamnatin Najeriya ba ta nuna wata alama ta kawo karshen zaman daliban a gida ba.

Tun a ranar 14 ga watan Fabrairu ne ASUU ta tsunduma yajin aiki, bisa zargin gwamnatin Najeriya da gaza cika alkawuran da ta dauka a yarjejeniyar da suka ƙulla, ciki har da batun inganta rayuwar malaman da kuma dambarwar shigar da kungiyar tsarin biyan albashi na IPPIS da gwamnatin ta fito da shi. A cewar BBC.

Ilimi

Kaduna:- Daliban Kuriga sun sha ki iskar ‘yanci

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da rahoton cewa an sako duka ɗaliban makarantar Kuriga da ƴanbindiga suka sace.

 

An sace ɗaliban firamare da na sakandare su kusan 287 a makarantarsu da ke ƙauyen Kuriga a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna fiye da makonni biyu da suka wuce.

 

Sanarwar da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya fitar ta ce an sako duka ɗaliban kuma suna cikin koshin lafiya.

 

Sanarwar ba tayi karin bayani ba game da irin matakan da aka bi wajen sako ɗaliban, sai dai gwamna Uba Sani ya nuna godiya ga shugaba Tinubu da mai bashi shawara kan tsaro da kuma sojojin Najeriya saboda irin rawar da suka taka wajen ganin an sako ɗaliban.

 

“Ba dare babu rana ina tattaunawa da Malam Nuhu Ribadu domin lalubo hanyoyin da za a bi wajen kubutar da daliban, kafin mu samu nasara,” in ji Uba Sani.

 

Galibinsu ɗaliban da aka sace ƴan shekaru biyar ne zuwa 18.

Continue Reading

Hangen Dala

Gaya Ajingi Albasu:- Dan majalisa ya raba kayan abinci

Published

on

Dan majalisar Tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu Dakta Ghali Mustafa Fanda ya fara rabon tallafin kayan abinci ga al’ummar kananan hukumomin uku.

 

Yayin rabon tallafin kayan abincin, Dakta Ghali Mustafa yace yayi rabon tallafin ne domin fara sauke nauyin al’ummar da yake wakilta.

 

” Wannan tallafi zamu bayar da shi ne domin fara sauke nauyin al’ummar da suka zabe mu, kuma wannan shi ne karon farko, kuma yayi daidai da bukatar al’umma a yanzu, shiyasa muka fara da tallafin kayan abinci”.

 

“A cikin wannan tallafi mutane kimanin dubu ashirin ne zasu amfana, wanda zamu bayar da buhunan Shinkafa da Gero da Garin masara.”

 

Haka kuma ɗan majalisar ya bayar da tallafin Naira miliyan ashirin ga matasan kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu.

 

Sai kuma ɓangaren dalibai mata, wanda shima a yau dan majalisar ya dauki nauyin karatun dalibai mata guda 60 a bangaren lafiya.

 

Haka kuma cikin jawabin nasa Hon Ghali ya kuma ce nan gaba kadan zai bayar da tallafin taki ga manoma, da kuma farfaɗo da dukkanin rijiyon burtsatse na kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu a wani mataki na samar da ruwan sha.

 

Da yake nasa jawabin mataimakin gwamnan Kano Kwamred Aminu Abdussalam Gwarzo wanda ya samu wakilcin mai baiwa Gwamna Shawara kan harkokin siyasa Hon Sunusi Surajo Kwankwaso kira yayi ga sauran wakilan al’umma da suyi koyi da Dakta Ghali Mustafa Fanda wajen ayyukan alkhairi da kuma jin kan al’umma.

 

Haka kuma Hon Sunusi Surajo ya yabawa dan majalisar bisa bayar da tallafin ga ƙananan hukumomin uku.

 

Taron dai wanda ya gudana a cikin Islamic Centre na karamar hukumar Gaya ya samu halartar manya, da kuma jagororin yankunan uku, kuma nan take Dan majalisar Tarayya Dakta Ghali Mustafa ya fara rabon tallafin

Continue Reading

Ilimi

Za’a daga likafar BMC zuwa Diploma – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin Kano tace nan bada jimawa ba za’a daga likafar makarantar koyon aikin jarida a matakin farko wato BMC ta Goron Dutse zuwa tsarin Diploma.

Mataimakin gwamnan Kano Kwamred Aminu Abdussalam ne ya tabbatar da hakan lokacin da yake jawabi a wurin taron da kungiyar tsaffin daliban makarantar suka shirya.

Kwamred Aminu Abdussalam ya kuma ce nan bada jimawa ba makarantar za’a daga matsayin karatun daga Certificate zuwa Diploma, kamar yadda makarantar ta bukata.

Kazalika yace gwamnatin Kano za ta cigaba da lura da dukkanin kayan koyo da koyarwa har ma da ababen hawa na hukumar ilimin manya ta Kano, wato Agency for mass Education wadda a cikin ta ake karatun na jarida.

Taron dai wanda shi ne karo na farko da gamayyar kungiyar daliban ta shirya tun bayan kafuwar makarantar shekaru 38 da ta gabata, ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da suka haɗar da Kwamishinan ilimi na Kano da Kwamishinan yada labarai da kwamishiniyar mata da mai baiwa gqamna shawara kan harkokin yada labarai.

Kazalika taron ya samu halartar Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero da tsaffin malaman makarantar da kuma shugabannin kafafen yada labarai na Kano.

A yayin taron dai shugaban kungiyar taaffin daliban Ismaila Ammai me Zare ya kaddamar da wani tsari na tallafawa makarantar da abin zama mai taken ( ka dawo da kujerar ka ).

Continue Reading

Trending