Connect with us

Manta Sabo

Da Duminsa: Kotu ta umarci APC ta mika sunan Machina maimakon Sanata Ahmed Lawal

Published

on

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Damaturu, ta umarci jam’iyyar APC da ta mika sunan Bashir Shariff Machina a matsayin dan takarar sanatan Yobe ta Arewa, bayan tabbatar da zaben fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar a ranar 28 ga watan Mayun 2022.

Mai shari’a Fadimatu Murtala, a cikin hukuncin da ta yanke yau a Damaturu, ta kuma soke zaben fidda gwani na ranar 9 ga watan Yunin 2022 wanda ya samar da shugaban majalisar dattawa, Ahmed Lawan.

Lauyan wanda ke dogara da shi na biyu Kolawale Balogun ya shaida wa manema labarai cewa, za a ba wa wanda yake karewa shawara kan mataki na gaba.

Manta Sabo

Zargin ɓata suna: Kotu ta bada Belin Ƴar TikTok Alpha Chales Borno

Published

on

Kotun Majistret mai lamba 17 karkashin jagoranci mai Shari’a Huda Haruna Abdu, ta bayar da belin matashiyar yar Tiktok din nan Alpha Charles, wadda Ƴan Sanda suka gurfanar a gaban bisa zargin ta da laifin ɓata suna.

Ƙunshin zargin ya bayyana cewar Alpha Charles, ta ɓata sunan Sadiya Haruna ta dandalin sada zumunta.

Yayin da aka karanta mata tuhumar ta musanta, kuma lauyoyin da suke kare ta sun roki beli, Inda kotun ta sanya ta a hannun beli a bisa sharadin mutum biyu da za su tsaya mata,

Kazalika, sharuɗan Belin sun bayyana cewa, dole ne masu tsayawar na ɗaya ya zama ɗan uwanta na jini, ɗayan kuma ma’aikacin gwamnati mai mataki na 16, idan ta tsere masu karbar belin zasu ajiyewa kotun Naira dubu ɗari biyar.

Sai dai lauyan Alpha ya bayyana wa kotun cewar, Sadiya Haruna ta ɗauki hoto da bidoyon Alpha a harabar kotun ta kuma yaɗa a dandalin Facebook, tare da wasu maganganu da suke zargi na batanci ne.

A don haka kotun ta nemi mai ƙara Sadiya Haruna, sai dai an neme ta sama ko ƙasa ba a ganta ba, an kuma umarci lauyanta da ya gabatar da ita.

Wakilin Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, kotun ta sanya ranar 28 ga wannan watan Afrilun da ake ciki na shekarar 2025, don ci gaba da sauraron shari’ar.

Continue Reading

Baba Suda

Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.

 

Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.

 

Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Continue Reading

Manta Sabo

Kotu ta yanke wa wasu mutane 5 hukuncin Kisa ta hanyar Rataya a Kano

Published

on

Babbar kotun jihar Kano, mai lamba huɗu karkashin jagorancin mai Shari’a Usman Na Abba, ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya akan wasu mutane 5, waɗanda kotun ta samu da laifin haɗa baki da kisan kai.

Tunda fari gwamnatin jihar Kano ce ta gurfanar da mutanen a gaban kotun, da ake zargin su da haɗa baki da kisan kai.

Ƙunshin zargin da ake musu tun da fari ya bayyana cewar, a ranar 3 ga watan 9 na shekarar 2023 wata mata Mai suna Nadiya Ibrahim ta bayyana wa mai gidanta Faisal Yahaya cewar, ta yi mafarkin cewar wata makociyarsu mai suna Tsahare Abubakar ta biyo ta da wuka, bayan da ta farka kuma sai ta kama rashin lafiya.

Har ila yau, ƙunshin tuhumar ya bayyana cewar, Faisal ya yi zargin Tsahare mayyace, don haka ya gayyato wasu matasa 4 su ka bi Tsahare har gona suka daddatsa ta har sai da rai ya yi halinsa.

A yayin sauraron Shaidu lauyan gwamnati Barrister Lamido Abba Soron Ɗinki, ya gabatar da shaidu 4, kuma a yau kotun ta ayyana cewar, ta gamsu da shaidun masu gabatar da kara.

Kotun ta ayyana hukunci kisa ta hanyar rataya akan mutanen masu suna Daluta Ibrahim, da Abudil-Aziz Yahaya, da Faisal Yahaya, da kuma Ahmad Ibrahim, sai Abdurrahman Yakubu.

Sai dai kuma wata mata da ake tuhuma ta 6 mai suna Nadiya Ibrahim, kotun ta sallame ta sakamakon an gano cewar lokacin da aka yi kisan kan ita tana gida a kwance bata da lafiya.

Kazalika, kotun ta kuma gargadi yan uwan Tsahare akan cewar kada su cutar da Nadiya domin kotun ta gano bata da laifi.

Wakilimmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, kotun ta kuma umarci Dagacin garin Ɗadin kowa da ke karamar hukumar Wudil, da su tabbatar an zauna lafiya akan wannan batu, har ma mai Shari’a Usman Na’Abba ya ce, ba a yin hukunci akan mafarki kuma idan wani ya faru da mutum sai ya tuntuɓi masana abin.

Continue Reading

Trending