Siyasa
APC ce za ta lashe zaben 2023 – Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa, jam’iyyar All Progressives Congress (APC) za ta lashe zaben shugaban kasa a 2023.
Buhari ya ce, APC ta yi sa’ar samun Tinubu a matsayin dan takararta na shugaban kasa.
Ya yi magana ne a kasar Birtaniya yayin da ya ke mayar da martani kan yiwuwar APC ta lashe zaben shugaban kasa a 2023.
Da aka tambaye shi kan yiwuwar APC na rashin yin nasara a 2023, Buhari ya ce: “Mene ne damar jam’iyyata ba za ta ci zabe ba? Za mu ci zabe.
“Tinubu, dan takarar shugaban kasa, sanannen dan siyasa a kasar nan, ya kasance gwamna na wa’adi biyu a jihar Legas, jihar da ta fi kowa arziki kuma jihar da aka fi ziyarta.
“Don haka, ina ganin jam’iyyar ta yi sa’ar samun shi ya zama dan takara.”
A watan Yuni, Tinubu ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, bayan ya doke mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo; Shugaban majalisar dattawa Ahmad Lawan da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi.
Tsohon gwamnan jihar Legas ya samu kuri’u 1,271, inda ya doke abokin hamayyarsa Amaechi wanda ya samu kuri’u 316.

Hangen Dala
Maja:- NNPP ta amince da tayin Atiku

Jam’iyyar NNPP ta yi maraba da kiran da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya yi na dunkulewar manyan jam’iyyun adawa don kwato mulki daga jam’iyyar APC mai mulki.
NNPP ta bayyana hakan ne a wani taron manema labarai da Shugaban jam’iyyar na kasa, Abba Kawu Ali, ya yi ranar Talata a Abuja.
Ali ya ce, “A kwanakin baya ne tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya yi kira ga manyan jam’iyyun adawa da su hade kai a matsayin hanyar da za a bi wajen ganin an dakile mulkin kama-kamarya da jam’iyyar APC mai mulki ke yi da kuma wanzar da Dimokuradiyya a kasar.
“Jam’iyyar NNPP tana ganin wannan kira na Alhaji Atiku Abubakar a matsayin kishin kasa kuma abin farin ciki ne wanda hakan yasa muke ganin wannan a wani mataki mai amfanarwa,” inji wani bangare daga cikin sanarwar.

Hangen Dala
Gwamnatin Kano ta ja hankalin al’umma Kan hukuncin da kotun daukaka Kara za ta yanke

Gwamnatin Jihar Kano ta bukaci al’ummar jihar da su kwantar da hankalinsu gabanin hukuncin kotun daukaka kara da za a yanke a gobe Juma’a.
A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Baba Halilu Dantiye, ya raba wa manema labarai a Kano a ranar Alhamis, ta hannun Sani Abba Yola, Daraktan ayyuka na musamman na ma’aikatar.
Sanarwar ta bukaci al’ummar jihar su guji tada tarzoma ko kalaman da za su tada hankali kafin da kuma bayan hukuncin kotun.
Dantiye, wanda ke mayar da martani kan hukuncin zaben gwamna da za a yi gobe da kotun daukaka kara a Abuja, ya jaddada bukatar jama’a su wanzar da zaman lafiya domin ci gaban jihar da kasa baki daya.
Ya kuma yi kira ga hukumomin tsaro da su zage damtse wajen ganin an tabbatar da doka da oda don tsare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.

Hangen Dala
Kotun daukaka Kara ta ayyana zaben kujerar Gwamnan zamfara a matsayin Wanda Bai kammala ba

Kotun ɗaukaka ƙara da ke zamanta a Abuja ta ayyana zaɓen gwamnan jihar Zamfara, a matsayin wanda bai kammala ba.
A hukuncin da ɗaukacin alƙalanta uku ƙarƙashin Mai shari’a Sybil Nwaka suka amince da shi, kotun ta soke halascin zaben Gwamna Dauda Lawal Dare na ranar 18 ga watan Maris din 2023.
Kotun da yammacin ranar Alhamis a Abuja, ta kuma bayar da umarnin sake gudanar da zaɓe a ƙananan hukumomin Zamfara uku, da suka haɗa da Maradun da Birnin-Magaji da kuma Bukkuyum.
Ta ce kotun sauraron ƙararrakin zaɓe ta jihar Zamfara, ba ta yi la’akari da hujjojin da masu ƙara suka gabatar ba – wato jam’iyyar APC .
Kotun ta kuma yi watsi da sakamakon da jam’iyyar APC da hukumar zaɓe ta ƙasa INEC suka bayar na ƙaramar hukumar Maradun.
Don haka ta umarci hukumar zabe (INEC) ta gudanar da sabon zabe a ƙananan hukumomin uku, inda ba a gudanar da zabe ba a baya, ko kuma ba a ƙidaya sakamakon wasu tashoshin zabe ba.
Dan takarar jam’iyyar APC a zaben watan Maris, Bello Matawalle ne sake kalubalantar hukuncin da karamar kotun zaben jihar Zamfara ta yanke, wanda ta kori shari’arsa bisa hujjar cewa ya gaza gabatar da gamsassun hujjoji.
Tsohon gwamnan na Zamfara, wanda a yanzu yake rike da mukamin karamin ministan tsaro, yana neman wa’adin mulki na biyu ne bayan karewar mulkinsa na tsawon shekara hudu.

-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai3 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi4 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya1 year ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi4 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano