Connect with us

Siyasa

APC ce za ta lashe zaben 2023 – Buhari

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa, jam’iyyar All Progressives Congress (APC) za ta lashe zaben shugaban kasa a 2023.

Buhari ya ce, APC ta yi sa’ar samun Tinubu a matsayin dan takararta na shugaban kasa.

Ya yi magana ne a kasar Birtaniya yayin da ya ke mayar da martani kan yiwuwar APC ta lashe zaben shugaban kasa a 2023.

Da aka tambaye shi kan yiwuwar APC na rashin yin nasara a 2023, Buhari ya ce: “Mene ne damar jam’iyyata ba za ta ci zabe ba? Za mu ci zabe.

“Tinubu, dan takarar shugaban kasa, sanannen dan siyasa a kasar nan, ya kasance gwamna na wa’adi biyu a jihar Legas, jihar da ta fi kowa arziki kuma jihar da aka fi ziyarta.

“Don haka, ina ganin jam’iyyar ta yi sa’ar samun shi ya zama dan takara.”

A watan Yuni, Tinubu ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, bayan ya doke mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo; Shugaban majalisar dattawa Ahmad Lawan da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi.

Tsohon gwamnan jihar Legas ya samu kuri’u 1,271, inda ya doke abokin hamayyarsa Amaechi wanda ya samu kuri’u 316.

Hangen Dala

Gaya Ajingi Albasu:- Dan majalisa ya raba kayan abinci

Published

on

Dan majalisar Tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu Dakta Ghali Mustafa Fanda ya fara rabon tallafin kayan abinci ga al’ummar kananan hukumomin uku.

 

Yayin rabon tallafin kayan abincin, Dakta Ghali Mustafa yace yayi rabon tallafin ne domin fara sauke nauyin al’ummar da yake wakilta.

 

” Wannan tallafi zamu bayar da shi ne domin fara sauke nauyin al’ummar da suka zabe mu, kuma wannan shi ne karon farko, kuma yayi daidai da bukatar al’umma a yanzu, shiyasa muka fara da tallafin kayan abinci”.

 

“A cikin wannan tallafi mutane kimanin dubu ashirin ne zasu amfana, wanda zamu bayar da buhunan Shinkafa da Gero da Garin masara.”

 

Haka kuma ɗan majalisar ya bayar da tallafin Naira miliyan ashirin ga matasan kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu.

 

Sai kuma ɓangaren dalibai mata, wanda shima a yau dan majalisar ya dauki nauyin karatun dalibai mata guda 60 a bangaren lafiya.

 

Haka kuma cikin jawabin nasa Hon Ghali ya kuma ce nan gaba kadan zai bayar da tallafin taki ga manoma, da kuma farfaɗo da dukkanin rijiyon burtsatse na kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu a wani mataki na samar da ruwan sha.

 

Da yake nasa jawabin mataimakin gwamnan Kano Kwamred Aminu Abdussalam Gwarzo wanda ya samu wakilcin mai baiwa Gwamna Shawara kan harkokin siyasa Hon Sunusi Surajo Kwankwaso kira yayi ga sauran wakilan al’umma da suyi koyi da Dakta Ghali Mustafa Fanda wajen ayyukan alkhairi da kuma jin kan al’umma.

 

Haka kuma Hon Sunusi Surajo ya yabawa dan majalisar bisa bayar da tallafin ga ƙananan hukumomin uku.

 

Taron dai wanda ya gudana a cikin Islamic Centre na karamar hukumar Gaya ya samu halartar manya, da kuma jagororin yankunan uku, kuma nan take Dan majalisar Tarayya Dakta Ghali Mustafa ya fara rabon tallafin

Continue Reading

Hangen Dala

Shugaban kasa ya bayar da umarnin bude Boda

Published

on

Shugaban kasa Asuwaju Bola Ahmad Tinubu ya bayar da umarnin bude iyakokin kasar nan.

Cikin sanarwar da ya fitar shugaban ya ce duk wata iyaka dake tsakanin Nigeria da jamhuriyar Nijar a gaggauta bude ta.

Karin bayani na nan tafe…

Continue Reading

Hangen Dala

An gurfanar na Ramat a gaban kotu

Published

on

Wasu yan jam,iyyar NNPP anan kano sun shigar da karar wani tsohon shugaban karamar hukuma.

Mutanen dai sun yi karar hon Abdullahi Garba Ramat tsohon shugaban karamar hukumar Ungogo, a gaban babbar kotun shariar muslinci ta birni.

Masu karar suna zargin Ramat da laifin tayar da hankalin al,imma ta hantar gayyato wasu yandaba suka tare musu hanya a lokacin yakin neman zabe sai dai Ramat din ya musanta zargin.

Mai sharia Ibrahim Sarki Yola ya aike da su wajen yansanda don a fadada bincike.

Alhaji Abubakar Iliyasu shine jagoran masu karar ya bayyana mana matsayarsu

Yanzu haka yansandan shahuci sun bukaci masu kara da su kawo gamsassun hujjoji akan da,awarsu.

Continue Reading

Trending