Manyan Labarai
Rikici ya barke a tsakanin Malaman Islmaiyya da ‘yan kwamiti

Hukumar Shari’a ta Jihar Kano ta ce ta samar da sulhu a tsakanin ‘yan kwamitin makaranatar Tarbiyatul Auwlad da kuma malaman makarantar dake unguwar Chirancin a karamar hukumar kumbotso.
Mai rikon mukamin shugabancin hukumar, Malam Bashir Ibrahim, ya bayyana hakan ne a wata takarda mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na hukumar, Sani Muhammad Sadiq, ya sanyawa hannu.
Ya na mai cewa” An samu cimma daidaiton ne bayan kiran bangarorin biyu da mu ka yi tare da sauraron su a hukumar ta shari’a kuma a ka samu fahimtar juna”.
Haka kuma anyi adu’o’in samun dorewar zaman lafiya a makarantar da jihar Kano dama Kasa baki daya.
Tun dai a baya ne Malaman makarantar suka yi yajin aiki a kan sauyawa makarantar suna zuwa Mahadi maimakon sunan ta na baya, Tarbiyatul Auwlad wanda idan malaman sun dauki mataki a kan dalibai dazarar sun aikata laifi, sai mai makarantar ya yi watsi tare da nuna bacin ran sa.
Haka zalika wannan matakin da malaman suka dauka wasu daga cikin iyayen daliban suka fito tare da nuna bacin ran su kan hukuncin dai na koyar da daliban a makarantar, wanda ta kai har sai da a ka tafi gaban hakimin Kumbotso domin ya samar da sulhu a tsakanin su.
Labarai
Marayu da marasa galihu na bukatar taimakon al’umma – Limami

Wani malamin Addinin musulunci a jihar Kano ya bukaci al’umma da su dage wajen taimakawa marayu da marasa galihu dake cikin al’umma.
Limamin masallacin juma’a na Bilal Bn Rabah da ke garin Taura a Jihar Jigawa Dakta Isah Salisu Yaro ne ya bayyana haka jim kadan bayan kammala bude sabon masallacin juma’a na Shu’aibu Ali, dake Unguwar Ayagi a cikin karamar hukumar Dala a nan Kano.
Ya ce, “Taimakawa addini abu ne da al’ummar musulmi ya kamata su rinka a ko da yaushe”. Inji Dakta Isah Salihu.
A na sa jawabin limamin masallacin Ustaz Kabiru Sani Salihu, kira ya yi ga al’umma da su zama masu yawan godiya ga Allah (S.W.T) a kan ni’imar da ya yi wa bayin sa.
Labarai
Rahoto: A guji amfani da matasa domin tayar da rigima a wajen zabe – Limami

Limamin masallacin juma’a na Shelkwatar rundunar ‘yan sanda da ke Bompai SP Abdulkadir Haruna ya bukaci shugabanni da su guji amfani da matasa wajen tayar da hankalin al’umma a wajen zabe.
SP Abdulkadir Haruna ya bayyana hakan ne jim kadan bayan idar da sallar Juma’a, yayin da ya ke yiwa wakilin mu Abba Isah Muhammad Karin gaske akan abinda hudubar ta kunsa.
Domin jin cikakken rahoton saurari wannan.
Labarai
Ya zama wajibi mu rinka yiwa tsofaffin sojoji addu’a – Ganduje

Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya ce ya zama wajibi a rika yiwa tsoffin sojoji addu’a saboda sadaukar da rayuwar su wajen tabbatar da ci gaban kasar su.
Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin bikin tunawa da tsoffin sojojin da suka hidimtawa kasa.
Ya ce, “Da dama daga cikin tsoffin sojoji sun rasa rayuwar su ne wajen ganin kasar nan ta zauna lafiya da kwantar da tarzoma adon haka ya zama lallai a rika tunawa dasu da Yi musu addu’a”. A cewar Ganduje.
Wakiliyar mu Zahrau Nasir ta rawaito cewa, an gudanar da faretin tunawa da tsoffin sojojin yayin taron.
-
Manyan Labarai11 months ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Nishadi1 year ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai11 months ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Nishadi1 year ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai12 months ago
Ba’amurkiya da masoyin ta sun hada cinkoso a kasuwar Sabon Gari
-
Nishadi1 year ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Labarai3 months ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Manyan Labarai12 months ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano