Connect with us

Labarai

 Kano: Yarinya ‘yar shekara biyu ta shiga kangin tallace-tallace

Published

on

Da safiyar yau Alhamis ne wasu matasa Sulaiman Abdullahi Bala da Amina Salisu su ka ga wata karamar yarinya dake unguwar Kwanar Jaba a Jihar Kano, ‘yar kimanin shekaru biyu ta na sayar da wainar filawa.

Matasan sun kawo yarinyar gidan rediyon Dala inda su ka bayyana takaicin su kan yadda yarinyar da sanyin safiya ta fito talla ko magana ba ta iya yi sosai.

Sulaiman Abdullahi ya ce, “Ina kan hanya ne, zan je in sayi wani abu a garin kwanar Jaba, sai naga an taru ina zuwa sai naga yarinya ce an zagaye ta ga kuma robar wainar filawa a hannunta da kuma kudi, na tambaya sai a ke ce min wannan yarinyar talla take, sai na ga wannan ma idan ka bata kudi ba za ta iya irgawa ba, ya za a yi mutum ya sayi abu kuma ta bashi canji? sanyi ma zai iya kama ta, nima abun ya ba ni tausayi”.

Naji kayi maganar sanyi wacce irin shiga ce a jikinta?

“Hijabi ne a jikinta, sai wata ‘yar riga sai dan takalmi. Naga kudi a hannunta kusan Naira Dari Biyu. Ni fatana a duba a gani wannan yarinyar ai ta yi karama. Akwai wadanda a wajen ma sun san ta, domin ta na kawo talla wajen su.” Inji Sulaiman

Ya kuma kara da cewa, “Iyayen ta su tsaya su duba, wannan ai, abun dubawa ne, yaro kamar wannan karama ce sosai cin zarafin yara ne”.

A nata bayanin Amina Salisu ta ce, “Mun kai yara makaranta, sai mu ka yi magana da wata zan karbi wani abu a hannun ta, muna zuwa sai muka ga taro ana ta korafi, wata yariyna ce karama take ta zuwa ta na kawo talla a cikin gida, shi ne abun ya ba ni tausayi na tsaya na ce gaskiya bai dace yarinya karama kamar wannan an bar ta tana talla, saboda haka na ce ya dace in kai ta inda za a tallafa mata”.

To kun nemi iyayen ta, ko kuji wane hali a ke ciki?

“Gaskiya bamu nema ba, abun da ya sa bamu nema ba saboda ance yarinyar in tayi laifi har a turken dabbobi a ke daure ta a dake ta. Ka ga ma hannun ta shaida ce karaya ce aka yi mata, kuma jikin ta in ka duba shaidar duka ne.” Inji Amina.

Wakilin mu Aliyu Wali, ya zanta da yarinyar ta na mai cewa, “Waina nake sayarwa, biyu Naira biyar, babarmu ta na gida, sunan ta Rabi, baban mu sunan sa Sani, ni kadai ce ba ni da kani, da safe nake fitowa talla, ina zuwa islamiyya, ba na zuwa boko”.

Naga ciwo a hannunki me ya ji miki ciwo?

“(Kuka) Wani yaro ne yaji min ciwo a unguwar mu ba abun da na yi masa”.

Mutanen da su ka tsince ta a unguwar ta Jaba sun kuma ce, za su mayar da ita gida ne sun kawo ta gidan rediyo ne domin a tallafa mata domin yara irin ta su ne wadanda a ke cutarwa a yi musu fyade, tare da sace su a sauya masu suna.

Wakilin mu Aliyu Wali da Abba Isah Muhammad, sun garzaya zuwa hukumar Hisba tare da yarinyar da kuma wadanda suka tsinto ta, a nan ne kuma hukumar ta bazama neman iyayen yarinyar domin an bi mata hakin ta. Sai dai a nan gaba zaku ji sauran labarin.

Hangen Dala

Rashin wuta: Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Published

on

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.

Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.

Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.

Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.

Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.

Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.

Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.

Continue Reading

Hangen Dala

Rashin wuta:- Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Published

on

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.

 

Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.

 

Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.

 

Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.

 

Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.

 

Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.

 

Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.

Continue Reading

Labarai

Ci gaba ba ya zuwa sai an samu haɗin kan al’umma – Dagacin Ja’en

Published

on

Dagacin garin Ja’en da ke ƙaramar hukumar Gwale a jihar Kano, Alhaji Isma’il Sa’ad Usman, ya ce hadin kai ne kaɗai zai kawo ci gaba ga kowa ce irin al’umma.

Dagacin ya bayyana hakan ne Jim kaɗan bayan wani taron masu Ruwa da tsaki na Garin Ja’en, wanda Hakimin Gundumar Ɗorayi Barde Kerarriya Alhaji Shehu Kabir Bayero ya shirya, aka gudanar a yankin Ja’en a ƙarshen makon da ya gabata.

“Dukkanin wani ci gaba ba ya zuwa har sai an samu haɗin kan kowa ne bangare na al’umma, “in ji Dagacin”.

Wakilin Dala FM Kano, Ahmad Rabi’u Ja’en ya ruwaito cewa, taron ya samu halartar dukkanin bangarori, na unguwannin Ja’en, da suka haɗar da kungiyar mafarauta da maharba dabma kungiyar malaman makaranta.

Continue Reading

Trending