Connect with us

Labarai

KAROTA ba ta da hurumin yi wa mutane tara a kan kullen Corona -Baba Jibo

Published

on

Wasu mutane a birnin Kano sun yi kukan cewar Jami’an hukumar KAROTA su na kama su a cikin masallacin Idi a yi musu tarar kudade har Naira dubu biyar.

Masu korafin dai sun bayyana cewar sakamakon dokar kulle Jami’an jami’an na yi mu su tara a cikin masallacin idi. A ida a ke yankewa masu babur hukuncin biyan tarar dubu uku yayin da mu su babur mai kafa uku a ke yanke masu hukuncin biyan tarar dubu biyar.

Wakilin mu Yusuf Nadabo Ismail ya kai ziyara masallacin Idin, ya kuma iske tarin masu babura wadanda su ke jiran a yanke musu hukunci a lokacin.

Harma wakilin na mu ya zanta da wasu daga cikin mutanen wadanda su ka bayyana yadda a ke yi mu su tara, Usaini Abdullahi mazaunin unguwar Gidan Zoo wanda ya ce” Na kawo wani mara lafiya zuwa asibitin Murtala kawai sai na ji kawai an kama ni a ka kai ni cikin filin Idi tare da cin tara ta”.

Shi kuwa wani matashi mai suna Magaji Idris cewa ya yi Na je ‘yan Lemon a kawo lemo zuwa cikin Fagge kawai sai wani jami’in KAROTA ya kama ni ya kai ni cikin masallacin Idi a ka kuma cini tarar dubu biyar.

Sai dai kakakin kotunan jihar Kano, Baba jibo ya ce”KAROTA ba su da hurumin yin tara a harkar kullen covid 19, domin kuwa wannan ba hurumin ta ba ne”.

Audio Player

Mun kuma tuntubi mai magana da yawun hukumar KAROTA Nabulisi Abubakar Kofar Na’isa wanda ya bayyana cewar” Wanda ya tabbata ya yi laifi kotu c eke da ikon ta ci tarar mutum kawai dai idan jami’an sun kama mutum za su kai su wajen kotun tafi da gidan ka a yanke mu su hukunci”.

Audio Player

Hangen Dala

Rashin wuta: Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Published

on

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.

Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.

Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.

Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.

Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.

Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.

Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.

Continue Reading

Hangen Dala

Rashin wuta:- Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Published

on

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.

 

Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.

 

Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.

 

Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.

 

Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.

 

Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.

 

Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.

Continue Reading

Labarai

Ci gaba ba ya zuwa sai an samu haɗin kan al’umma – Dagacin Ja’en

Published

on

Dagacin garin Ja’en da ke ƙaramar hukumar Gwale a jihar Kano, Alhaji Isma’il Sa’ad Usman, ya ce hadin kai ne kaɗai zai kawo ci gaba ga kowa ce irin al’umma.

Dagacin ya bayyana hakan ne Jim kaɗan bayan wani taron masu Ruwa da tsaki na Garin Ja’en, wanda Hakimin Gundumar Ɗorayi Barde Kerarriya Alhaji Shehu Kabir Bayero ya shirya, aka gudanar a yankin Ja’en a ƙarshen makon da ya gabata.

“Dukkanin wani ci gaba ba ya zuwa har sai an samu haɗin kan kowa ne bangare na al’umma, “in ji Dagacin”.

Wakilin Dala FM Kano, Ahmad Rabi’u Ja’en ya ruwaito cewa, taron ya samu halartar dukkanin bangarori, na unguwannin Ja’en, da suka haɗar da kungiyar mafarauta da maharba dabma kungiyar malaman makaranta.

Continue Reading

Trending