Connect with us

Labarai

Atiku ya buƙaci Birtaniya ta kawo ɗauki a kan tsaro da tattalin arziki

Published

on

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi tsokaci kan kara hadin gwiwa tsakanin gwamnatin Birtaniya da Najeriya, wajen lalubo hanyoyin da za a magance matsalolin daza su amfani kasashen biyu.

Sanarwar da mai taimaka masa a kan kafafen yaɗa labarai, Abdulrasheed Shehu ya rabawa manema labarai, ya rawaito cewa, Atiku, ya bayar da shawarar ne a lokacin da tawagar babbar hukumar Burtaniya karkashin jagorancin High Catriona Laing ta gana da Atiku a gidansa da ke Abuja a jiya.

A yayin ganawar Atiku da bakinsa sun tattauna batutuwa da dama da suka shafi tsaro, ilimi, noma, tattalin arziki da kuma samar da hadin kan kasa a Najeriya.

Babban Kwamishinan ya bayyana cewa, ganawar da tsohon mataimakin shugaban kasar wani bangare ne na ci gaba da gudanar da ayyukan gwamnatin Burtaniya, domin inganta dimokuradiyya da sahihin zabe a Najeriya.

Da yake mayar da martani, Atiku ya nuna jin dadinsa ga tawagar da suka ba da lokacin gudanar da taron, ya kuma bayyana cewa, “dangantakar da ke tsakanin Najeriya da Birtaniya na da tarihi mai dimbin yawa, kuma yana da muhimmanci kasashen biyu su yi amfani da wannan damar wajen inganta al’amuran da suka shafi kasashen biyu tare da damuwa da juna.”

Wazirin Adamawa ya jaddada cewa, yana sa ran kasar Ingila za ta taka rawar gani wajen tabbatar da dorewar dimokuradiyya a Najeriya, kuma yana da yakinin cewa, zaben shugaban kasa a 2023 zai kasance cikin gaskiya da adalci.

A kan batun rashin tsaro, ya yi tir da halin da ake ciki a kasar, ya kuma nemi taimakon Birtaniya musamman a fannin horarwa da musayar bayanan sirri.

Da yake magana game da tattalin arziki, tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce, idan aka ba shi dama ya jagoranci al’amuran Najeriya, zai tare da sauran abubuwa, zai kawar da tsarin musayar kudade da yawa tare da rage haraji don karfafa masana’antu na gaske da kuma bunkasa jari na gaske. Ya kuma yi alkawarin bunkasa harkar noma, domin samar da ayyukan yi ga al’ummar kasar nan.

Bugu da kari, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP ya bayyana damuwarsa kan yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i ke yi da kuma rikicin da ke faruwa a fannin ilimi.

Ya yi alkawarin aiwatar da gyare-gyare a fannin ilimi, gami da sake farfado da shirin ba da lamuni na kudi ga daliban Najeriya. 

Hangen Dala

Rashin wuta: Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Published

on

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.

Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.

Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.

Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.

Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.

Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.

Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.



Continue Reading

Hangen Dala

Rashin wuta:- Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Published

on

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.

 

Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.

 

Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.

 

Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.

 

Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.

 

Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.

 

Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.



Continue Reading

Labarai

Ci gaba ba ya zuwa sai an samu haɗin kan al’umma – Dagacin Ja’en

Published

on

Dagacin garin Ja’en da ke ƙaramar hukumar Gwale a jihar Kano, Alhaji Isma’il Sa’ad Usman, ya ce hadin kai ne kaɗai zai kawo ci gaba ga kowa ce irin al’umma.

Dagacin ya bayyana hakan ne Jim kaɗan bayan wani taron masu Ruwa da tsaki na Garin Ja’en, wanda Hakimin Gundumar Ɗorayi Barde Kerarriya Alhaji Shehu Kabir Bayero ya shirya, aka gudanar a yankin Ja’en a ƙarshen makon da ya gabata.

“Dukkanin wani ci gaba ba ya zuwa har sai an samu haɗin kan kowa ne bangare na al’umma, “in ji Dagacin”.

Wakilin Dala FM Kano, Ahmad Rabi’u Ja’en ya ruwaito cewa, taron ya samu halartar dukkanin bangarori, na unguwannin Ja’en, da suka haɗar da kungiyar mafarauta da maharba dabma kungiyar malaman makaranta.



Continue Reading

Trending