Connect with us

Siyasa

A shirye na ke na yi aiki da abokan tafiya ta – Atiku

Published

on

Wasu ’yan takarar shugabancin kasar nan da suka fafata a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP da ya gabata, sun yi alkawarin goyon bayan takarar Atiku Abubakar.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka wa Atiku kan harkokin  yada labarai, Abdurasheed Shehu ya fitar, ya ce, tsofaffin ‘yan takarar shugaban kasa karkashin jagorancin Mohammed Hayatudeen, sun yi wa Atiku biyayya a lokacin da suka kai masa ziyara. Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da Kalu Chikwendu, Tarry Oliver, Dele Momodu da Charles Ugwu.

Hayatudeen ya bayyana cewa, sun zo ne domin taya mai rike da tutar jam’iyyarsu murnar nasarar da ya samu a zaben fidda gwani da kuma yi masa fatan alheri a zabe mai zuwa, tare da fatan Atiku ya samu nasarar lashe zaben.

Cif Dele Momodu ya bayyana mahimmancin samun dukkanin masu neman shugabancin kasar nan, wanda a cewarsa hakan zai tabbatar da samun nasara ga jam’iyyar a rumfunan zabe.

A cikin kalamansa ya ce, “Dole ne dukkan masu son tsayawa takara su hadu wuri guda don ganin jam’iyyar ta kai ga nasara, kuma na yi imanin cewa PDP na da mafi kyawun damar lashe zaben shugaban kasa a 2023”.

Ya bukaci masu ruwa da tsaki su shiga tsakani, ya kuma yi kira ga kowa da kowa da su marawa jam’iyyar baya domin samun nasara.

Ya yi nuni da cewa, “kowane korafe-korafe a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar, yana da kyau kowa ya taru; don haka hadin kan jam’iyyar zai haifar da nasarar zabe ga kowa da kowa.”

Mace daya tilo da ta tsaya takara a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP da ya gabata, Mrs Tarry Oliver, a takaice nata jawabin, ta bayyana cewa, a matsayinsu na ‘yan takara na farko, suna tuntubar dukkan takwarorinsu tare da fatan kowa ya hau kujerar naki domin isar da jam’iyyar a dukkan zabukan. .

Ta bayyana tsayuwarta cewa, tsarin jam’iyyar zai karfafa tsarin hadin gwiwa wanda zai hada da shigar mata da matasa wanda zai baiwa jam’iyyar damar mayar da hankali kan yakin neman zabe.

A cewarta, jam’iyyar PDP iyali daya ce mai hadin kai, ta kuma baiwa ‘yan Najeriya tabbacin cewa duk wani abu da ke faruwa a cikin jam’iyyar na cikin gida ne wanda a karshe za a warware shi cikin ruwan sanyi.

A nasa martanin dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bayyana jin dadinsa da ziyarar taya murna da suka kai masa tare da yaba musu bisa yadda suka amince da sakamakon zaben fidda gwani na shugaban kasa.

Atiku ya ba su tabbacin cewa, a shirye yake ya yi aiki da su a matsayin abokan tarayya, ta hanyar tabbatar da nasarar jam’iyyar PDP a zaben 2023 mai zuwa.

Ya kuma jaddada muhimmancin yin aiki tare a matsayin hadin kai a fafutukar ganin an ceto Najeriya daga mummunan shugabanci.

Tsohon Mataimakin Shugaban kasar ya bayyana cewa aikin kwato kasar ba aikin mutum daya ba ne, hakki ne na hadin gwiwa.

Atiku ya bayyana cewa yayin da lokacin yakin neman zabe ke kara gabatowa, ya sa ran za a kara tattaunawa da kungiyar.

Hangen Dala

Lauyoyin gwamnatin Kano sun bukaci a kamo Ganduje

Published

on

Babbar kotun jaha mai lamba 7 karkashin jagorancin mai sharia Amina Adamu ta sanya karfe biyu da rabi na ranar yau dan bayyana matsayarta akan batun gurfanar da tsohon gwamnan kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa da wasu mutane.

A zaman kotun na yau lauyoyin gwamnatin jaha sun bayyana wa kotun cewa an sadar da sammace ga wadanda ake kara ta hanyar kafafen yada labarai kamar yadda kotun ta yi umarni tun a baya amma wadanda ake kara basu samu damar halartar kotun ba dan haka ya roki ko dai a kamo su ko kuma kotun ta ci gaba duk da cewar basa gaban kotun.

Sai dai lauyan wanda ake kara na 6 barrister Nuraini Jimo SAN ya yi suka inda ya bayyana cewar kotun ta dakata tun da sun daukaka kara ya kuma bayyana cewar kotun bata da hurumi sannan kunshin tuhume-tuhumen yana dauke ta kura-kurai.

Kotun zata bayyana matsayarta a yau da rana.

Tun da farko gwamnatin kano ta yi karar Ganduje da mutane 6 bisa zargin almundahana akan kudi sama da Naira Biliyan 4 da aka yi zargin sun sayarda wasu filaye sun raba kudin.

Continue Reading

Labarai

Da Dumi Dumi:- EL Rufai ya kai karar majalisar dokoki

Published

on

Tsohon Gwamna jahar Kaduna Mal. Nasir elrufai ya Maka majalisar Dokokin jahar Kaduna a gaban Kotu a bisa bata Masa Suna da majalisar tayi na cewa Gwamnatin sa ta sace kudaden jahar da Suka naura naira miliyan dubu Dari Hudu.

Tsohon Gwamna ya shigar da karar ce, a Gaban babbar kotun taraiyya dake NDA Kaduna a safiyar Laraban nan 26 ga watan Yuni 2024.

Inda ya bukaci Kotun data tursasa majalisar ta bashi hakuri a bainar jama’a, sakamakon Kazafin da Yan majalisan Suka yi masa da mukarraban Gwamnatinsa data gabata.

 

Karin bayani na nan tafe….

Continue Reading

Siyasa

Zauren jam’iyyun haɗin kan kasa IPAC sun cire shugaban jam’iyyar LP na Kano Abdullahi Raji daga cikin tafiyar su 

Published

on

Sakataren zauren jam’iyyun haɗin kan kasar nan, IPAC na ƙasa reshen jihar Kano, kuma shugaban jam’iyyar APM na Kano Honarable Nuhu Idris, ya ce sun cire shugaban jam’iyyar LP na jihar Kano Abdullahi Raji daga cikin tafiyar su ta IPAC, baki ɗaya.

Sakataren na IPAC, Nuhu Idris ya ce sun dauki wannan mataki ne bisa yadda Rajin ke amfani da kungiyar CUPP, da rusassun jam’iyyun kasar nan suka samar a baya, a dan haka, duk wata jam’iyyar dake da rijista a yanzu na ƙarƙashin IPAC.

Ya kuma ce dokar da ta kafa IPAC, ba ta bai wa ɗan kowacce jam’iyya damar shiga hurumin wata jam’iyyar ba kamar yadda Rajin ke ƙoƙarin yi a rikicin dake faruwa a jam’iyyar APC a nan jihar Kano.

Shugaban jam’iyyar APM, ɗin Honarable Nuhu Idris, ya ce sun cire Rajin daga tafiyar ta IPAC ne, sakamakon wata sanarwa da ya fitar, ya ce, ka da hukumar zaɓe INEC, ta yi watsi da shugaban mazaɓar Ganduje, wanda hakan ba dai-dai ba ne a dokance, dan haka, suka fitar da shi daga cikin tafiyar tare da sanar da shugabancin jam’iyyar sa na kasa.

Continue Reading

Trending