Connect with us

Manyan Labarai

Corona Virus: Liman ya ja hankali a kan cutar

Published

on

Limamain masallacin ma’aiki dake garin Madinatul’munauwara, Abdul- bril bn Aiwan Affabiti ya ja hankalin al’ummar duniya da su zamo masu komawa ga Allah kan dukkanin al’amuran su ta yadda za a samu saukin bullar annobar cututtuka, irin su Corona Virus da take sarke numfashi, wanda yanzu haka take addabar al’ummar duniya musamman a kasar Sin wato china.

Limamain ya bayyana hakan ne ta cikin hudubar sallar juma’a wanda ya gabatar yau a masallacin na ma’aiki dake garin Madina.

Da yake fassara hudubar ta yau jim kadan bayan kammalata, Malam Aminu Kidir idris wanda shi ne limamin masallacin Usman Bn Affan dake unguwar Kuntau a karamar hukumar Gwale ta bakin limamin ya ce,” Baya ga daukan matakan kariya da masana lafiya suke bayyanawa, a yawaita addu’o’I, zikirai da istigifari sune za su taimaka wajen shawo kan matsalar”. A cewar limamin ta fasarar sa.

Fassarar wani bangare kenan na hudubar msallacin ma’aiki dake garin Madinatul’munauwara, wanda limamin na yau Abdul- Baril Bn Aiwan Affabiti, wanda limamain masallacin Usman Bn Affan dake unguwar Kuntau a karamar hukumar Gwale a jihar Kano, Malam Aminu Kidir Idris ya fassara.

Manyan Labarai

Hukumar Shari’a ta shirya kawo ƙarshen ƙwacen Waya a Kano

Published

on

Hukumar Shari’a ta jihar Kano, ta ce za ta tunkari matsalar ƙwacen Waya haɗin gwiwa da dukkan shugabannin kasuwannin wayoyi da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro da hukunci a jihar Kano, don kawo ƙarshen matsalar.

Kwamishina na biyu a hukumar Shari’a ta jihar Kano, Sheikh Ali Ɗan Abba, ne ya bayyana hakan a shafin sa na sada zumunta a ranar Asabar, biyo bayan yadda ake ci gaba da fuskantar ƙalubalen ƙwacen waya a birnin Kano, lamarin da ke sanadiyyar rayukan jama’a daga masu ƙwacen wayar, tare da asarar dukiyoyi.

Sheikh Ali Ɗan Abba, ya kuma ce, a makon da za a shiga ne Hukumar shari’a ta jihar Kano, za ta bayyana irin tsauraran matakan da za ta ɗauka a kan wannan masifar da ta gallabi al’ummar jihar, wato matsalar fashin Waya da Makami.

Tashar Dala FM Kano, ta ruwaito cewa, Sheikh Ɗan Abba, ya kuma yi addu’a akan lamarin, inda ya ce “Allah ya taimake mu ya kawo mana ƙarshen wannan masifar ta fashin Waya da makami a Kano”.

Wannan dai na zuwa ne yayin da al’ummar Kano, da masana harkokin tsaro, ke ci gaba da kiraye-kiraye ga mahukunta da su ƙara tashi tsaye wajen yin abinda ya dace don kawo ƙarshen ƙwacen waya, da faɗan Daba, da kuma shaye-shayen kayan maye, a jihar, la’akari da yadda lamarin ya ke damun jama’a.

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Labarai

Real Madrid ta kaddamar da Alexander

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta ƙaddamar da ɗan wasa Trent Alexander Arnold a yau a matsayin ɗan wasan ta

Inda shugaban ƙungiyar Flerontino Perez yace yau suna matuƙar Farin ciki kasancewar sun mallaki babban ɗan wasan baya a duniya.

 

Shima ɗan Wasa Arnold ya bayyana cewa yana cikin farin ciki kuma mafarkin sa ya cika na zama ɗan Wasan Madrid a yau.

Continue Reading

Trending